fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Ƴan fashin teku sun yi garkuwa da ma’aikatan jirgi 16

Ƴan fashin teku sun yi garkuwa da ma’aikatan jirgi 16

 

Mamallakan jirgin ruwan ƙasar Denmark da masu fashi a teku suka ƙwace a mashigar Guinea a makon da ya gabata sun ce ƴan fashin sun tsere sun bar jirgin, inda suka tafi da ma’aikatansa guda 16.

 

Sai dai an samu nasarar kuɓutar da wasu da ke cikin jirgin mai suna Monjasa Reformer.

 

Waɗanda suka mallaki kwale-walen sun bayyana a ranar Talata cewa wasu ma’aikatan jirgin biyar sun samu mafaka a cikin wani ɗaki jirgin lokacin da ƴan fashin suka afka cikinsa.

Karanta wannan  Tinubu ya gana da sarakunan gargajiya a fadarsa

 

Ƴan fashin sun ƙwace ikon jirgin ne a ɓangaren yammacin birnin Pointe-Noire da ke Jamhuriyar Kongo.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *