fbpx
Saturday, June 10
Shadow

2023: Nageriya na bukatar shugaba irin Tinubu – Kungiyar Malaman addinin Kirista

Kungiyar Malaman addinin Kirista reshen Kudu-maso-Kudu ta Najeriya ta jaddada goyon bayan ga tsohon Gwamnan Jihar Legas Mista Bola Tinubu.

Malaman sun bayyana cewa Najeriya na bukatar dan siyasa mai girman kamar Tinubu domin ya zama shugaban kasar.

Malaman sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da babban kodinetan, Joseph Francis na Delta da mataimakin kodineta, Apostle Chris Ebhodaghe na Edo, suka bayar ga manema labarai a Benin ranar Litinin.

Kungiyar ta bukaci mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da su tabbatar da cewa Tinubu ya samu tikitin jam’iyyar.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *