Friday, January 17
Shadow

Aƙalla mutum 95 sun ràsù a girgizar ƙasa a China

Wata mummunar girgizar ƙasa ta afku a kusa da iyakar Tibet da Nepal.

Aƙalla mutum 95 ne aka tabbatar da mutuwarsu, sannan sama da 130 sun jikkata a girgizar, wadda ta afku a ranar Talata.

Girgizar ta kuma ƙetara zuwa yankin Nepal da ke ƙasar Indiya, wanda ke maƙwabtaka da Tibet na ƙasar China.

Girgizar ƙasar ta lalata gine-gine a birnin Shigatse na Tibet, lamarin da ya sa jama’a su riƙa kwararowa kan tituna domin tsira.

Tuni sojojin ƙasar suka fara aikin ceto, inda suka aika jirage marasa matuƙa zuwa wani yanki mai nisa a kusa da tsaunin Everest.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: Atiku, Kwankwaso Da Peter Obi Sun Fara Tattaunawa Domin Hadewa Waje Daya Don Tunkarar Zaben 2027

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *