ALLAH SARKI: Ta Koma Tara Yashi Tana Sayarwa Domin Ciyar Da ‘Ya’ya Hudun Da Mijinta Ya Rasu Ya Bar Mata A Kaduna
… tana bukatar taimakon jama’a
Daga Aliyu Ahmad
Malama Binta Lawal kenan dake yankin Rigasa a jihar Kaduna, wadda ta dukufa da sana’ar debo yashi daga rafi tana sayarwa domin ciyar da ‘ya’ya hudun da mijinta ya rasu ya bar ta da su.

Jama’a wannan mata tana bukatar tallafi duba da sana’ar tara yashin iya lokacin damuna ne da ruwa ke kawo shi, idan rani ya yi babu damar tara yashin. Don haka idan da hali jama’a tallafa mata da jari domin ganin ta kama wata sana’ar da zai dore saboda ta rufawa kanta da ‘ya’yanta marayu asiri.
Ga masu bukatar yin magana da Malama Binta Lawal kai tsaye don karin bayani daga gare ta, ga lambarta; 08067905129
Ko kuma a ziyarce ta a Madina road by Abuja road North Rigasa Kaduna.