fbpx
Saturday, June 10
Shadow

An gurfanar da wata matashiya a gaban kotu bisa zargin mutuwar wata mata mai shekaru 85 a Adamawa

Wata yarinya ‘yar shekaru 15 a jihar Adamawa ta gurfana a gaban kotu bayan da ta amsa laifinta da ta yi wa wata tsohuwa ‘yar shekara 85 duka har lahira.

An tattaro cewa lamarin ya faru ne a ranar Litinin 8 ga watan Afrilu.

Matashiyar mai suna Happy David da ake zargin ta yi amfani da sanda ne, ta kai farmaki gidan matar mai suna Gama Jatau da ke unguwar Tambo a karamar hukumar Girei, inda ta lakada mata duka bisa zargin maita.

An garzaya da mamacin zuwa asibiti a Jabbi Lamba a karamar hukumar Girei inda aka tabbatar da rasuwar ta.

Bayan mutuwar tsohuwar, an gurfanar da yarinyar a gaban kotu inda ta amsa laifinta.

Daga nan ne babban alkalin kotun ya dage zaman kotun zuwa ranar 26 ga Mayu, 2022.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *