fbpx
Thursday, June 8
Shadow

An kashe mutane sama da 80 a makon da ya gabata a Najeriya

Rahotanni sun bayyana cewa, Mutane akalla 113 ne aka kashe a Najeriya a makon da ya gabata.

 

A satin dake gaban wanda ya gabata kuwa, mutane 48 ne aka kashe a kasarnan.

 

Na farko shine wanda aka kashe mutane kusan 40 a Owo dake jihar Ondo.

 

Sai kuma mutane 6 da aka kashe a unguwar Sabo da Hausawa ke ciki a jihar ta Ondo Wanda na zuwane a matsayin harin daukar fansa.

 

A jihar Sokoto kuwa, mutane da dama ne aka kashe a garuruwan Gebe da Alkammu.

Karanta wannan  Bidiyo: Anga 'yansandan Najariya na cin zarafin wasu matasa

 

Sai kuma a Kaduna an kashe mutane 32, kamar yanda Premium times ta ruwaito.

 

A jihar Kwara kuwa, mutane 2 ne aka kashe.

 

A babban birnin tarayya, Abuja kuwa an kashe wani manomi aka tafi da dabbobinsa.

 

 

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *