fbpx
Saturday, June 10
Shadow

An kashe shugaban wani kauye da mutane 14 a sabon harin da aka kai Kaduna

‘Yan Bindiga sun kashe shugaban wani kauye da mutane 14 a jihar Kaduna a wani sabon hari da suka kai jihar.

 

Lamarin ya farune a Kakura dake karamar hukumar Chukun ranar Lahadi inda hakan ya jefa mutane da yawa cikin tashin hankali.

 

An kashe shugaban kauyen Isiaku Madaki da wasu mutane 14 a harin da ake tunanin na ramuwar gayyane.

 

Yawancin mazauna garin Kakura kabilar Gbagi ne. Ranar Asabar ne aka nada Isiaku Madaki shugabancin kauyen inda a ranar Lahadi kuma, wasu da ba’a san ko su wanene ba suka kasheshi.

 

Hakan yasa aka kaiwa wani garin Fulani hari dan daukar fansa inda a canne aka kashe karin mutane 14n.

 

Zuwa yanzu dai hukumomin jihar dana ‘yansanda basu ce komai ba akan lamarin.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *