Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bude wani gurin sayar da abinci na zamani a Abuja, jiya Asabar da ya sawa suna, Chicken Cottage, Atikun ya bayyana cewa zai bude irin wannan gurin sayar da abincin a sauran jihohin Najeriya ta yanda hakan zai samarwa da da yawan ‘yan kasarnan ayyukan yi.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Ya kara da cewa kuma manomanmu da masu sarrafa kayayyaki daban-daban anan cikin gida Najeriya suma zasu karu da wannan sabon kasuwanci daya bude tunda zaau kawo kayansu a siya ayi amfani dasu ba tare da an fita neman kasashen wajeba.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});