Sojojin Najeriya sun tarwatsa tawagar dalibai masu zanga-zanga a jihar Ondo.
Kalli bidiyon a kasa
https://www.instagram.com/tv/CdqgDCBsyr4/?igshid=YmMyMTA2M2Y=
Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas tare da hadin gwiwar ‘yan uwanta jami’an tsaro a ranar Talata sun lalata wasu miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 10.
Mataimakin kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka, DCP Ahmed Kotangora ne ya jagoranci tawagar zuwa rumbun da ke Ewu-Elepe da ke wajen Ikorodu a jihar Legas, domin lalata magungunan.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, ‘yan sanda, jami’an NDLEA, NAFDAC, Neighborhood Watch da kuma jami’an yaki da cin hanci da rashawa ne suka sa ido kan atisayen.
DCP Kotangora, wanda ya wakilci kwamishinan ‘yan sanda a jihar Legas, CP Abiodun Alabi, ya ce atisayen ya bi umarnin kotu na lalata miyagun kwayoyi da tawagar ‘yan sanda ta Rapid Response Squad suka kwato a jihar a watan Afrilu.
Wani faifan bidiyo da ke nuna lokacin da wata waya ta makale a hannun barawo bayan ya sace ta a daya daga cikin gidaje a Nairobi, an yada shi ta yanar gizo.
A cewar wani ganau da ya raba bidiyon a TikTok, wayar ta makale a hannun barawon ne bayan da ya sace ta.
Mutane sun yi niyar Tara masa gajiya amma sun kasa hakan bayan da suka lura da cewa wayar da ya sace ta makale a hannunsa.
An danganta lamarin da asirin tsafi.
Kalli bidiyon a kasa....
https://www.instagram.com/reel/Cdoe2FoFJdc/?utm_source=ig_web_copy_link
Wata kotun majistare da ke zamanta a Ilesa a jihar Osun, a ranar Litinin din da ta gabata ta tasa keyar wasu da ake zargin barayi bisa laifin satar na’urar taranfoma da kudinsu ya kai N700,000 a Owa Obokun na Ijeshaland, fadar Oba Adekunle Aromolaran.
Wadanda ake zargin, Owolabi Abimbola mai shekaru 33, Sulaiman Mutiu, 25, Samson Oluwafemi, 25, da sauran su yanzu haka suna fuskantar tuhume-tuhume hudu kan laifin da suka aikata.
A cewar dan sanda mai gabatar da kara, Insfekta Adigun Kehinde, igiyoyin taranfoma da aka sace mallakin IBEDC reshen Ilesa ne.
A hukuncin da ya yanke, alkalin kotun, A.O Awodele, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 18 ga watan Mayu, sannan ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wadanda ake kara a hannun ‘yan sanda.
Jami’an hukumar ‘yan sandan farin kaya (DSS), reshen jihar Ogun, sun cafke wani kasurgumin dan fashi da makami da ake zargi da yi wa al’ummar Ota ta’addanci a karamar hukumar Ado-Odo/Ota ta jihar.
Wanda ake zargin, Elijah Adeogun aka Killer, an kama shi ne da misalin karfe 2.25 na daren ranar Litinin, 16 ga watan Mayu, a unguwar Araromi Estate, Iyesi, Ota, biyo bayan takardar koke da iyalan Adelupo na Ipetu Baba Ode suka rubuta ta hanyar Iju-Ota.
A cewar jaridar Nigerian Tribune, koken ya kunshi zargin cewa Adeogun ne ke da alhakin kisan gillar da aka yi a ranar Litinin 17 ga watan Nuwamba, 2021, kan wani lamari na fili tare da wasu mutane shida.
An ci gaba da cewa, wata tawagar dabara ta rundunar ta gudanar da wani samame na musamman wanda ya kai ga cafke Adeogun tare da wani...
An kashe ‘yan bindiga da dama yayin da jami’an tsaro na hadin gwiwa suka dakile wasu hare-hare a kananan hukumomi uku da ke jihar Neja
Dakile hare-haren ya biyo bayan kiran gaggawa da rundunar ta samu daga mazauna garuruwan, inda nan take suka isa wajen kuma sukai nasara akan yan bindigar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Wasiu Abiodun, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Minna a ranar Lahadi, 15 ga watan Mayu.
A halin da ake ciki, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Monday Bala Kuryas, ya jagoranci tawagar karfafa dabarun tun daga Minna zuwa Sarkin-Pawa, karamar hukumar Munya kuma an dawo da zaman lafiya.
Wasu dalibai masu kare martarba fiyayyen halitta, Annabi Muhammadu (SAW) sun kashe tare da Kone wata daliba Kirista har lahira bayan da ta zagi annabi Muhammadu (SAW) a cikin kwallejin ilimi ta Shehu Shagari da ke jihar Sakkwato.
A halin yanzu ana bayar da sanarwar rufe makarantar har sai baba ta gani.
Kalli bidiyon a kasa...
https://www.facebook.com/100008100669198/posts/3200718476874810/?app=fbl
Tsohon shugaban majalisar dattawa kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Ken Nnamani, ya bayyana yadda ake cewa wasu kungiyoyin suna sayen fom din tsayawa takarar shugaban kasa na jam’iyyar ga wasu ‘yan takara a matsayin “babban karya”.
Da yake magana a gidan talabijin na Arise TV a yau 12 ga Mayu, Nnamani ya ce ikirari na cewa kungiyoyin tallafi da dama sun siya fom ga dan takarar da suka fi so duk karya ne saboda wa su daga cikin su ba su da kudin da za su biya hayar gidajen da suke zama. Ya ce dole ne a dakatar da lamarin nan take.
Jami’an hukumar hana fataucin mutane ta kasa (NAPTIP) reshen jihar Anambra tare da hadin gwiwar hukumar shige da fice ta kasa reshen jihar Anambra, a ranar Laraba 11 ga watan Mayu, sun kama wani da ake zargi da safarar yara kanana tare da ceto wata karamar yarinya da yake kokarin zuwa da ita a kasar Dubai.
Wanda ake zargin wanda ke zaune a Onitsha, tare da hadin gwiwar ‘yan kungiyarsa dake jihar Edo da kuma Dubai, ya dauki yarinyar daga jihar Edo zuwa jihar Anambra.
An kama wanda ake zargin ne a ofishin shige da fice a lokacin da yake kokarin samo fasfo na Najeriya domin ya fita da yarinyar zuwa Dubai. A halin da ake ciki, hukumar ta NAPTIP ta kai yarinya zuwa wani gida mai tsaro yayin da ake ci gaba da bincike.
Wani faifan bidiyo na wani jami'in kwastam na Najeriya yana mari wani hadimin gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa ya bayyana a yanar gizo.
Dan rajin kare hakkin dan Adam, Harrison Gwamnishu, ya raba bidiyon a daidai lokacin da jami'in kwastam ya mari Mista Samson Nwachukwu a kan babbar hanyar Benin/Agbor a ranar Asabar, 7 ga Afrilu, a gaban abokin aikinsa da wani jami'in soja.
A cikin faifan bidiyon, ana iya jin dan sandan a fusace yana tambayar wanene Mista Samson Nwachukwu bayan ya shaida masa cewa shi mataimaki na musamman ne ga gwamnan jihar Delta kafin ya yi masa mari. Bidiyon ya ƙare tare da jami'in soja yana gaya wa jami'in kwastam ya "sake wannan mutumin."
Ko da yake, Gwamnishu bai bayyana abin da ya kai ga faruwar lamarin ba, amma ya sha alwashin nema wa Mista Nwachu...