fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Author: Ahmad A

Duk wanda muka yiwa auren gata a Kano ya saki matar ba tare da izini hizba ba to sai ya mayarwa gwamnati kudin data kashe masa, Daurawa

Duk wanda muka yiwa auren gata a Kano ya saki matar ba tare da izini hizba ba to sai ya mayarwa gwamnati kudin data kashe masa, Daurawa

Uncategorized
Shugaban hukumar ta Hizba Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa yace dole ne, cikin waɗanda zasu shiga Auren gata da Gwamnatin Kano zatai kwanan nan, su kiyaye wajan sakin wacce aka Aura musu. Duk abinda ya faru kai da matar ka, matsawar ba zaku dai daita ba, kuzo Hizba domin a gyara komai amma mutum baida ikon sakin matar sa haka kawai dole sai yazo Hizba anji me ya faru domin a gyara ɓarakar. Yace A wannan (Auren Gata) da zamu yi, duk mijin da ya saki matar sa haka kawai kuma ba tare da sanin Hizba ba, zai biya Gwamnati kuɗin da ta kashe masa da duk abinda akai masa. Meye ra'ayin ku?  
Kungiyar kwadago ta kasa zata tsunduma yajin aiki kan matsin rayuwa da ake ciki da cire tallafin man fetur

Kungiyar kwadago ta kasa zata tsunduma yajin aiki kan matsin rayuwa da ake ciki da cire tallafin man fetur

Breaking News
Ƙungiyar ƙwadago ta NLC a Najeriya ta sanar da anniyar shiga yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyu kan matsin da 'yan ƙasar ke ciki sakamakon janye tallafin fetur.   NLC ta ce za ta gudanar da yajin aikin ne a ranakun Talata da Laraba mai zuwa.   A ranar da aka rantsar da shi, shugaba Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin man fetur, yanayin da ya haifar da tsadar man daga naira 197 zuwa naira 617.   NLC ta nuna ƙin amincewa da matakin gwamnati da aiwatar da zanga-zanga a faɗin ƙasar.   Shugaba Tinubu ya sha ganawa da 'yan ƙwadagon a kokarin ganin an cimma daidaito.
Ba zamu dagawa sojojin Nijar kafa ba, dole su bada mulki

Ba zamu dagawa sojojin Nijar kafa ba, dole su bada mulki

Siyasa
Ƙungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka, Ecowas ta jadadda cewa babu batun ɗaga kafa ko bai wa sojojin Nijar dogon lokaci kafin mayar da ƙasar kan turbar dimokuraɗiyya. A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, Ecowas ta ce an ja hankalinta kan wasu rahotanni da ke cewa ta ba da shawarar wa'adin miƙa mulki, wanda kuma wannan labari ba daga wajenta ya fito ba. Ecowas ta ce rahotan da ake yaɗawa har a kamfanin dillancin labarai na AFP, babu gaskiya a cikinsa. Ƙungiyar ta sake jadadda bukatarta ga sojojin Nijar da su mayar da Mohamed Bazoum kan mulki nan take. Kafin wannan sanarwa an ji yo shugaban Ecowas, Bola Ahmed Tinubu yana cewa babu batun a sakarwa sojoji Nijar mara. Bola Tinubu ya ce: "ina ma laifin sojojin da suka yi juyin-mulki su yi koyi da mulkin tsohon shugaban mulkin soja ...
Rashin Shugabanci na Gari ke kawo ta’addanci A jihohin Arewa maso Yamma ~Cewar Kashim Shettima

Rashin Shugabanci na Gari ke kawo ta’addanci A jihohin Arewa maso Yamma ~Cewar Kashim Shettima

Siyasa
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce rashin shugabanci na da alakar kai tsaye” kan yawaitar ‘yan fashi da garkuwa da mutane a shiyyar arewa maso yamma. Shettima ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya karbi bakuncin kungiyar hadin kan ‘yan kasuwa, masana’antu, ma’adanai, da noma na jihohin Arewa, CONSCCIMA, a fadar shugaban kasa da ke Abuja. Shugaban kungiyar Dalhatu Abubakar ne ya jagoranci kungiyar. Arewa maso yamma ta ƙunshi jihohi bakwai: Jigawa, Kaduna, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto, da Zamfara. Musamman jihohin Zamfara, Katsina da Sokoto sun kasance wuraren da ‘yan fashin suka addabi jama’a, lamarin da ya janyo sace mutane da kashe-kashe a ‘yan kwanakin nan. Shettima ya ce masu ruwa da tsaki a yankin arewa baki daya “dole ne su koma kan hukumar zana zane, su ...
KADUNA: Gwamna Uba Sani ya fara aikin gina makarantu na zamani guda 62 a Kaduna

KADUNA: Gwamna Uba Sani ya fara aikin gina makarantu na zamani guda 62 a Kaduna

Siyasa, Uncategorized
KADUNA: Gwamna Uba Sani ya fara aikin gina makarantu na zamani guda 62 a Kaduna Daga Wakiliya Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani a lokacin da yake aza harsashin ginin babbar makarantar sakandare a Nasarawan Rigachikun, a karamar hukumar Igabi, ya ce wannan ginin da ya kafa na nuni da cewa za a fara gina makarantu 62 a fadin jihar. Wakiliya ta ruwaito Gwamnan na cewa manufar gina makarantun shi ne a tabbatar da cewa kowane yaro yana zuwa makaranta. Sanata Uba Sani ya bayyana cewa, kowace makaranta da za agina za a wadata ta da kayayyakin more rayuwa da makarantun zamani ke buƙata, da ajujuwa, da dakunan gwaje-gwaje, da wuraren gudanar da ayyuka, da dakunan taro, da kuma bandakuna masu kyau da suka dace da zamani #100DaysOfGovUbaSani
‘Rabon tallafi ya haifar da tashin farashin shinkafa a Najeriya

‘Rabon tallafi ya haifar da tashin farashin shinkafa a Najeriya

Uncategorized
Matakin da gwamnatin Tarayyar Najeriya da jahohi ke ɗauka na sayen kayan abinci domin rarrabawa a matsayin tallafi ya haifar da tashi kayan abinci a kasuwanni. Rahotanni na nuna cewa 'yan kasuwa da dama na bayyana cewa buƙatar sayen kayan abincin da masu kwangila ke daɗa yi shi ne ya haifar da wannan lamari, ga shi kuma an samu ƙarancin shigo da abinci a kasuwanni. Tun bayan da Hukumar da ke lura da tattalin arzikin Najeriya ta fitar da sanarwa a ranar 7 ga watan Agusta, gwamnatin tarayya ta amince a fitar da naira biliyan 5 domin sayen abincin da za a tallafawa talakawa, aka soma faɗawa wannan yanayi.
Yan Bindiga Śun Ķòñé Mùťàñè Bìýù Da Ŕàñśu Cikin Mota A Jihar Katsina

Yan Bindiga Śun Ķòñé Mùťàñè Bìýù Da Ŕàñśu Cikin Mota A Jihar Katsina

Tsaro
Yan Bindiga Śun Ķòñé Mùťàñè Bìýù Da Ŕàñśu Cikin Mota A Jihar Katsina Daga Comr Nura Siniya Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai, sun kashe mutum biyu ta hanyar ƙoné su a cikin mota, kan hanyar da ta tashi daga Batsari zuwa Jibia a jihar Katsina. Wani mazaunin yankin wanda ya buƙaci a sakawa sunansa, ya shaida wakilin RARIYA cewa, ƴan bindigar sun tare motar ne, tsakanin hanyar Batsari zuwa Jibia inda suka bankawa motar wuta da mutanen biyu a ciki suka mutu har lahira. Al'amarin rashin tsaro yana ta ƙara ta'azzara a ƴan ƙwanakin nan musanman a ƙaramar hukumar Batsari, inda a kowane rana sai ƴan ta'addan sun kashe mutane sun yi garkuwa da manoma zuwa daji, don neman kuɗin fansa. Lamarin ya faru ne, a ranar Lahadi 6, ga watan Agusta 2023.