
Duk wanda muka yiwa auren gata a Kano ya saki matar ba tare da izini hizba ba to sai ya mayarwa gwamnati kudin data kashe masa, Daurawa
Shugaban hukumar ta Hizba Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa yace dole ne, cikin waɗanda zasu shiga Auren gata da Gwamnatin Kano zatai kwanan nan, su kiyaye wajan sakin wacce aka Aura musu.
Duk abinda ya faru kai da matar ka, matsawar ba zaku dai daita ba, kuzo Hizba domin a gyara komai amma mutum baida ikon sakin matar sa haka kawai dole sai yazo Hizba anji me ya faru domin a gyara ɓarakar.
Yace A wannan (Auren Gata) da zamu yi, duk mijin da ya saki matar sa haka kawai kuma ba tare da sanin Hizba ba, zai biya Gwamnati kuɗin da ta kashe masa da duk abinda akai masa.
Meye ra'ayin ku?