Sama da sojoji dubu huɗu n suka takarawar gani a faretin da aka yi a yau a fadar Buckingham.
Sarki da Sarauniya sun fito gefen matattakala da ke sama suna kallon yadda ake take ƙasa.
Sun sha shewa daga wajen rundunoni daban-daban na dakaru.
Tsohon Shùgaban Ƙasar Nàjeriya Malam Umaru Musa Ya Cika Shèkaru 13 Dà Rasüwa
Daga Anas Saminu Ja'en
A yau Juma'a 5 ga watan Mayun 2023 ne tsohon shugabar Najeriya Marigayi Umaru Musa Ƴar'Adu'a, adalin mai kishin talawa ya cika shekaru goma 13 cif da rasuwa, Allahu Akbar shekara kwana.
Tabbas an yi babban rashi a Najeriya, Allah ubangiji ya jiƙan sa ya kai rahama kabarin sa ya yafe masa kurakuran sa, tare da mu da sauran magabatan mu, Amin Ya Allah.
Shin da me za ku fi tunawa da Marigayi Umaru Musa Yar'Adua?
ALLAHU AKBAR: Wannan shi ne matashi Hassan daga kasar Fakistan, me shekaru 15 a duniya, Shi ne matashin da ya tseratar da sama da rayukan mutane dubu biyu a wata makaranta a kasar Fakistan.
Yayin da wani 'Dan kunan bakin wake ya yi yunkurin danna Bam a wata makaranta, Hassan shine Wanda ya rungume shi suka yi mutuwar kasko.
Mahaifiyar Hassan tayi farin ciki da samun wannan labari, ta ce, hakika Yarona yayi kyakyawar karshe, domin ya tseratar da rayukan dubun-dubatan mutane, Allah kasa Aljannah ce makomarsa.
Ku taya mu yada wannan rubutu don taya shi fatan samun Rahamar Allah.
SÒ GAMOÑ JINÍ: Wani Matashí Musulmí Zai Yí Wuf Da Jarumàr Shirin Dadiñ Kowà Dùk Da Cèwa Ita Ba Musulmà Bace
Saràh Aloysius da akafi sani dà Stephanie ta Shirin Dadin Kowa ta walaffa hotoñ ta da Nasir na Dadin Kowa a shafinta na Facebook.
Ta wallafa a cikin harshen Turanci cewa "Ina farin ciki da yin haka, nakuma kasance dakai har Abada aminina"
Ciki harda wallafa wasu alamomi na Aure da soyayya kamar haka: 💍🔐💝👩❤️💋👨
📸 Sarah Aloysius
ZUWA GA MASU SON AURENA: Zan Aure Ka Idan Ka Cika Dukkan Waɗan Nan Sharuɗan, Safara'u Ta Gindaya Tsauraran Sharuɗɗa Ga Masu Son Auren Ta
Shaharriyar ƴar Kannywood kuma mawaƙiyar nan Safara'u Yusuf (Safaa), ta gindaya wasu tsaurarn sharuɗa ga duk wanda yake da buƙatar don aurenta.
Na farko dole mu yi yarjejeniya a rubuce kasa hannu nima in sa, cewar bayan ka aureni za ka barni in cigaba da sana'a ta wato rawa da waƙa.
Na biyu idan ba za ka barni ba to za ka bani jarin naira miliyan 100 domin in fara zuwa Dubai ina siyo kaya ina siyarwa.
Na uku dole ka bani kyautar gida a Kaduna da Abuja da kuma motar hawa wacce ta kai darajar naira miliyan 15.
Idan ka ga za ka iya to ka ajiye min number wayarka zan kira ka.
"Don Allah masoyana ku taya ni tura wannan saƙ...
Haaland ko Messi: Ba zai yiyu a alakanta Messi da wani dan wasa ba, ban tana ganin irinsa ba amma ina fatan Haaland ya zama kamarsa>>Pep Guardiola.
Kocin kungiyar Firimiya ta Manchester City, Pep Guardiola wanda ya horas da Messi a kungiyar Barcelona yace Messi shine dan wasan duniya.
Wannan ba shine karo na farko da babban kocin ya bayyana hakan ba.
Yace bai tana ganin makamancinsa ba amma yana fatan shima Haaland ya zama kamar Messi watarana dan hakan zai amfane su.
Ya bayyana hakan ne yayin da ake tambayarsa tsakanin Messi da Haaland waye babban dan wasa.
Halima Dangote Diya a wajen hamshakin attajirin Afrika-Aliko Ɗangote.
An haifi Halima Aliko Dangote ( a kwaryar birnin Kano a Nigeria) 'yar kasuwa ce 'yar Najeriya, mai bayar da agaji wa mutane da dama,
Haka zalika Ita ce Babban Darakta na Gidauniyar Aliko Dangote da Dangote Industries Limited. Tana kuma aiki a hukumar Dangote Group.
Malama Halima Aliko-Dangote a halin yanzu ita ce babbar Darakta mai kula da harkokin kasuwanci a rukunin masana’antu na Dangote Industries Limited, inda take da alhakin gudanar da ayyukan raya kasa da aiwatar da ayyukan Dangote.
DAKTA NA’IMA IDRIS LIKITA ABAR ALFARIN ARÈWA DAMA NAHÍYAR AFRIKA GABA DAYÀ
DAGA Bashir Abdullahi El-bash
Addinin Musulunci wayayyen addini ne wanda ya ba wa dukkan al'umma maza da mata damar neman ilimi da gudanar da ayyukan cigaban rayuwar al'umma.
Tun farkon zuwan Addinin Musulunci, mata sun samu damar sanin ilimin likitanci da kuma yi wa marasa lafiya maza da mata magani musamman ma a wurin yaƙi.
A zamanin Manzon Allah SAW an samu mace likita mai suna Rufayda Bint Sa'ad Al-Aslamiyya. A lokacin yaƙin Badar ranar 13 Ga Watan Mach, 624 CE ita ce ta yi wa musulmai mayaƙa magani kan raunukan da su ka samu. Rufaida ta samu mafi yawan iliminta na likitanci a wurin mahaifinta Sa'ad Al-Aslami wanda masanin kiwon lafiya ne.
Sai kuma Al-Shifa Bint Al-Quraishiyya Al-Adawiya...