fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Author: hutudole

Me gadi ya dirkawa ‘yan mata 3 ciki

Me gadi ya dirkawa ‘yan mata 3 ciki

Uncategorized
Hankula sun tashi a makarantar Queen’s Convent School in Awka Dake jihar Anambra bayan da me gadin makarantar ya dirkawa dalibai 3 ciki.   Duka daliban da yawa cikin suna ajin SS3 ne.   Me gadin dai ya fara aiki ne watanni kadan da suka gabata kuma yana da shekaru sama da 30 kuma ya fito ne daga jihar Akwa-Ibom.   Jaridar Punchng tace zuwa yanzu dai ba'a san matakin da makarantar zata dauka akan me gadin ba.   Wata malama a makarantar ta bayyana cewa basa goyon bayan daukar matashi a matsayin me gadi amma hukumar makarantar taki yadda.   Gashinan yanzu abinda ba'a so ya faru.   Wasu iyaye dai sun yi barazanar cire 'ya'yansu daga makarantar.
Matan Shehu Ibrahim Inyass nawane

Matan Shehu Ibrahim Inyass nawane

Uncategorized
Kana da tambayar matan shehu ibrahim inyass nawane? Mafi ingancin amsa itace, matan Shehu Ibrahim Inyass 4 ne.   Akwai wasu ikirare-ikirare dake yawo cewa ya auri mata sama da 4 amma mafi ingancin bayani shine matansa 4 ne.   Daga ciki kuwa akwai 'yar Najeriya, Sayyada Bilqis wadda 'yar jihar Kogi ce.   Akwai kuma sayyada Fatimatou, sai kuma Sayyada Afiyatou, Akwai kuma Sayyida A'isha wadda rahotanni suka bayyana cewa, itace babba a cikin matan nasa.   Hakanan wasu rahotanni sun bayyana cewa 'ya'yansa 75, kuma ya rasu yana da shekaru 75, hakanan ya wallafa litattafai 75.   Saidai wasu rahotannin sun ce 'ya'yansa 100 kuma ba'a tantance iya yawan litattafan da ya rubuta ba.    
Yare nawane a Najeriya: Karanta Amsar Dalla-Dalla

Yare nawane a Najeriya: Karanta Amsar Dalla-Dalla

Uncategorized
Kana da tambayar yare nawane a najeriya? Ga amsarka kamar haka, Najeriya na daya daga cikin kasashen Duniya dake da yaruka mafiya yawa.   Akwai yaruka 500 a Najeriya.   Babban yaren aiki a Najeriya shine turanci, saidai ba'a cika amfani dashi a kauyuka ba.   Misali a yankin Arewa, anfi amfani da yaren Hausa, hakanan a yankin Kudu maso yamma anfi amfani da yaren Yarbanci, sai kuma a yankin kufu maso gabas an fi amfani da yaren Inyamuranci.   Ga wasu daga cikin yarukan: Abanyom Abon Abua Acipa, Eastern Acipa, Western Aduge Afade Agatu Agoi Agwagwune Ahan Ajawa Ake Akita Akpa Akpes Akum Alago Alege Alumu-Tesu Ambo Amo Anaang Anca Angas Arabic, Shuwa Arigidi Ashe ...
Hankula sun tashi saboda saboda yawaitar satar mazakutar maza a jihar Cross River

Hankula sun tashi saboda saboda yawaitar satar mazakutar maza a jihar Cross River

Uncategorized
Hankulan mutane sun tashi sosai a jihar Cross River saboda yawaitar rahotannin satar mazakutar maza.   Lamarin yasa maza suka rika yawo da namijin goro.   Gwamnatin jihar ta fitar da sanarwar cewa rahotannin satar mazakutar karyane.   Hakanan hukumar 'yansandan jihar itama ta fitar da sanarwar cewa satar mazakutar karyace.   Amma duk da haka mutanen jihar sun ki amincewa da karyata rahotannin.   Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa an samu akalla mutane 15 da aka ce lamarin ya faru dasu.   Wasu bayan an sace mazakutar tasu, ana dawo musu da ita.   An dai kama wasu da ake zargi da aikata lamarin, inda aka tashi da dukansu,  saidai zuwan jami'an tsaro ya tseratar dasu.
Baka isa kawa sarakunan Arewa haka ba, Sarkin Yarbawa ya soki Obasanjo kan wulakanta sarakunan Yarbawa

Baka isa kawa sarakunan Arewa haka ba, Sarkin Yarbawa ya soki Obasanjo kan wulakanta sarakunan Yarbawa

Uncategorized
Oluwo of Iwoland, Oba Abdulrasheed Adewale Akanbi Ya caccaki tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo kan wulakanta sarakunan yarbawa.   Obasanjo dai a wajan taron bude jami'ar Ladoke Akintola University of Technology College of Agriculture dake jihar Oyo ya soki sarakunan yarbawa saboda kin tashi tsaye su girmamashi bayan da ya hau kan mumbari.   Obasanjon ya umarci sarakunan da su mike su girmamashi inda kuma suka aikata hakan.   Saidai Oba Abdulrasheed ya bayyana cewa hakan cin fuskane ga sarakunan.   Yace da sarakunan Arewa ne bai isa ya musu haka ba, sannan kuma su ba sojoji bane da za'a rika tilastasu suna abinda basu sa kansu ba.
An gano wani mugun likita a Arewacin Najeriya dake sacewa mutane kodarsu a Asibintinsa, zuwa yanzu ya sace kodojin mutane 7

An gano wani mugun likita a Arewacin Najeriya dake sacewa mutane kodarsu a Asibintinsa, zuwa yanzu ya sace kodojin mutane 7

Uncategorized
Rahotanni daga yankin 'Yanshanu na karamar hukumar Jos North a jihar Filato na cewa hankula sun tashi matuka saboda gano wani likita da ake zargin ya sace kodojin mutane da dama a asibitinsa.   Sunan dai Asibitin Murna Hospital, sannan sunan me Asibitin Dr Noah Kekere.   Shugaban yankin na 'Yanshanu, Alhaji Jamilu Baba ya tabbatarwa da jaridar Tribune da wannan labari.   Yace duk mutanen da aka taba yiwa aiki a Asibitin yanzu suna zuwa ana duba musu kodarsu.   Inda yace zuwa yanzu an gano an sace kodar mutane akalla 7.   Yace an gano lamarinne bayan da wata mata ta je likitan ya mata aikin cire cutar appendix, saidai bata daina fama da rashin lafiya ba.   Koda lamarin yayi kamari sai mijinta ya bata shawarar gwada asibitin J...
Hotunan wanda aka kashe: ‘Yan Bindiga sun kashe mutane 15 da sace wasu 32 a jihar Kaduna

Hotunan wanda aka kashe: ‘Yan Bindiga sun kashe mutane 15 da sace wasu 32 a jihar Kaduna

Uncategorized
Rahotanni daga kudancin jihar Kaduna na cewa mutane 15 ne aka kashe sannan aka sace wasu 32 a wani hari da aka kai a garin Dogon Nama dake karamar hukumar Kajuru ta jihar. Akwai mutane da dama da aka ruwaito cewa sun jikkata.   Lamarin ya farune da safiyar ranar Juma'a kamar yanda Sahara Reporters ta ruwaito.   Maharan sun kuma bankawa gidaje da dama wuta, an zargi cewa fulanine.  
‘Yar wasan Tennis ta kasar faransa ta ce kocinta ya mata fyade sau 400, kalli hotunan

‘Yar wasan Tennis ta kasar faransa ta ce kocinta ya mata fyade sau 400, kalli hotunan

Uncategorized
'Yar wasan Tennis ta kasar Faransa, Angelique Cauchy ta zargi kocinta, Andrew Geddes da cewa ya mata fyade har sau 400.   Tace ya fara mata fyade tun tana da shekaru 12 ne.   Tace wasu lokutan yakan mata karyar cewa wai tana da cutar kanjamau.   Matar me shekaru 36 a yanzu tace kocin nata wanda a yanzu haka yake tsare inda aka mai daurin shekaru 18 saboda fyaden da yawa wasu mata a baya tace akwai sanda ya taba mata fyade sau 3 a rana.   Tace wani lokacin ta kan ji kamar ta kashe kanta.