fbpx
Saturday, March 25
Shadow

Author: hutudole

Hukumar ‘yansanda ta baiwa ‘yan Najariya shawarar kulle layukansu da lambobin sirri saboda wata sabuwar dabarar ‘yan ta’adda

Hukumar ‘yansanda ta baiwa ‘yan Najariya shawarar kulle layukansu da lambobin sirri saboda wata sabuwar dabarar ‘yan ta’adda

Uncategorized
Hukumar 'yansanda ta baiwa 'yan Najariya shawarar kulle layukansu ta hanyar amfani da lambobin sirri.   Kakakin 'yansandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin ne ya bayyana haka.   Yace an gano wasu barayi dake satar sim su kwashewa mutum duka kudin dake akawun dinsa na banki.   Yace wanda kawai basa iya kwashewa kudi shine wanda ya kulle layin wayarsa da lambobin sirri.   Dan hakane suke baiwa mutane shawarar daukar wannan mataki.    
Bamu nemi a soke zaɓen Kano ba – Masu sanya ido kan zaɓe

Bamu nemi a soke zaɓen Kano ba – Masu sanya ido kan zaɓe

Uncategorized
Bamu nemi a soke zaɓen Kano ba - Masu sanya ido kan zaɓe Gamayyar ƙungiyoyi da suka sanya ido a zaɓen Gwamnan Kano sun nemi jama'a su yi watsi da wani labari da ake yaɗawa wai sun nemi a soke zaɓen Kano. Ƙungiyoyin sun ce ba su da alaƙa da kowace jam'iyya su suna aiki ne don jama'a. Sun kuma ce za su ɗauki mataki kan waɗanda suka yi amfani da sunansu wajen yaɗa labarin ƙarya.
Ba Gwamnan da ya taimaki Kannywood kamar Kwankwaso>>Fitaccen Daraktan fina-finan Hausa Umar UK

Ba Gwamnan da ya taimaki Kannywood kamar Kwankwaso>>Fitaccen Daraktan fina-finan Hausa Umar UK

Uncategorized
Fitaccen Daraktan fina-finan Hausa Umar UK ya ce, ba a taba Gwamnan da ya taimaki Kannywood kamar Kwankwaso ba. UK ya ce, babu dalilin da wani dan Kannywood zai ki goyon bayan tafiyar tsohon Gwamna. A cewarsa Kwankwaso ya yiwa Kannywood riga da wando ta hanyar mayar da su makaranta a zamanin mulkinsa. https://youtu.be/JsriJzr49Ic Ga dai bayaninsa.
HOTUNA: Sanata Kwankwanso ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Maragayi Sani Abacha, bisa rasuwar ɗansu Abdullahi Sani Abacha, wanda ya rasu a makwannin baya. Maryam Abacha matar Maragayi Sani Abacha ce ta tarbe su a gidansu da ke Abuja

HOTUNA: Sanata Kwankwanso ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Maragayi Sani Abacha, bisa rasuwar ɗansu Abdullahi Sani Abacha, wanda ya rasu a makwannin baya. Maryam Abacha matar Maragayi Sani Abacha ce ta tarbe su a gidansu da ke Abuja

Siyasa
HOTUNA: Sanata Kwankwanso ya kai ziyarar ta'aziyya ga iyalan Maragayi Sani Abacha, bisa rasuwar ɗansu Abdullahi Sani Abacha, wanda ya rasu a makwannin baya. Maryam Abacha matar Maragayi Sani Abacha ce ta tarbe su a gidansu da ke Abuja.
Ban ce ba zan ba Tinubu Mulki ba>>Shugaba Buhari

Ban ce ba zan ba Tinubu Mulki ba>>Shugaba Buhari

Uncategorized
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya karyata rade-radin dake yawo cewa, wai yace ba zai baiwa zababben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu mulki ba.   Hakan ya fito ne daga bakin kakakin shugaban kasar, Malam Garba Shehu.   Garba Shehu yace waccan magana ta kanzon kurege ce.   Yace kwamitin da zasu karbi mulki da wanda zasu bayar suna ganawa kusan a kullun dan tabbatar da cewa mika mulkin ya tafi yanda ya kamata.
RAMADAN: Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Domin Saukakawa Ma’aikata

RAMADAN: Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Domin Saukakawa Ma’aikata

Uncategorized
RAMADAN: Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Domin Saukakawa Ma'aikata Daga Abubakar Shehu Dokoki Gwamnatin jihar Jigawa, ƙarƙashin Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ta rage wasu awanni, domin sauƙaƙa ayyuka ga ma'aikatan jihar, tareda samun cikakken lokacin gudanar da ibadar watan na Ramadan. Shugaban ma'aikata na jihar Hussain Ali kila yatabbatar da wannan al'amari, inda yace yanzu ma'aikatan zasu riƙa zuwa wajen aiki ne daga ƙarfe tara na safe (9am) zuwa ƙarfe uku na yamma (3pm), a maimakon tashi ƙarfe biyar na yamma (5pm) kamar yadda yake abaya, wannan yashafi ranakun aiki na ranar Litinin har zuwa Alhamis. Ya ƙara da cewa a ranar juma'a kuma, ma'aikatan zasu fita aiki ƙarfe tara na safe (9am) akuma tashi ƙarfe ɗaya na rana (1pm), kamar Yadda aka saba. A karshe ya...