
Da Gangan Aka Kirkiri Kungiyoyin Ta’addanci Irin Su Boko Haram Da Masu Garkuwa Da Mutane Don Tada Hankulan Al’umma Saboda A Sace Dukiyar Kasa>>Mejo Hamza Almustapha
Da Gangan Aka Kirkiri Kungiyoyin Ta’addanci Irin Su Boko Haram Da Masu Garkuwa Da Mutane Don Tada Hankulan Al’umma Saboda A Sace Dukiyar Kasa, Cewar Mejo Hamza Almustapha
Daga Bappah Haruna Bajoga
Dogarin Marigayi tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha, wato Mejo Janar Hamza Almustapha yace, da gangan aka kirkiri kungiyoyin 'yan ta'adda kamar Boko Haram da masu garkuwa da mutane don tada hankalin al'umma saboda sace arzikin kasa.
Hamza Almustapha yayi wannar magana, da kuma sauran wasu dumbin maganganu a kan lamuran kasar nan musamman na tsaro a sashen Hausa na BBC a cikin Shirin Gane Mini Hanya.
Ya kara cewa yankin Dajin Sambisa na jihar Borno akwai ma'adanan kasa da ake diba ake tafiya da su, kuma a yankin Zamfara ma da sauran wasu yankuna so ake a share mutanen wajen a z...