fbpx
Friday, March 31
Shadow

Author: wakiliya F.

Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya kafa Kwamitin karɓar mulki daga Gwamna Ganduje 

Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya kafa Kwamitin karɓar mulki daga Gwamna Ganduje 

Uncategorized
Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya kafa Kwamitin karɓar mulki daga Gwamna Ganduje   Hakan na cikin wata sanarwar da Kakakinsa Malam Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar da yammacin Jumu'ar nan.   Ga sunayen ƴan Kwamitin kamar haka.   1. Sen. AB Baffa Bichi, PhD Chairman 2. Prof. Hafiz Abubakar Member 3. Hon. Shehu Wada Sagagi Member 4. Hon. Umar Haruna Doguwa Member 5. Hon. Ahmad Garba Bichi Member 6. Dr Ali Haruna Makoda Member 7. Barr Maliki Kuliya Member 8. Barr. Haruna Isa Dederi Member 9. Dr. Danyaro Ali Yakasai Member 10. Engr. Muhammad Diggol Member 11. Dr Ibrahim Jibrin Provost Member 12. Sheikh Aminu Daurawa Member 13. Dr. Labaran Abubakar Yusuf Member 14. Pro...
Ƴan fashin teku sun yi garkuwa da ma’aikatan jirgi 16

Ƴan fashin teku sun yi garkuwa da ma’aikatan jirgi 16

Uncategorized
Ƴan fashin teku sun yi garkuwa da ma'aikatan jirgi 16   Mamallakan jirgin ruwan ƙasar Denmark da masu fashi a teku suka ƙwace a mashigar Guinea a makon da ya gabata sun ce ƴan fashin sun tsere sun bar jirgin, inda suka tafi da ma'aikatansa guda 16.   Sai dai an samu nasarar kuɓutar da wasu da ke cikin jirgin mai suna Monjasa Reformer.   Waɗanda suka mallaki kwale-walen sun bayyana a ranar Talata cewa wasu ma'aikatan jirgin biyar sun samu mafaka a cikin wani ɗaki jirgin lokacin da ƴan fashin suka afka cikinsa.   Ƴan fashin sun ƙwace ikon jirgin ne a ɓangaren yammacin birnin Pointe-Noire da ke Jamhuriyar Kongo.
Kwamitin yaƙin zaɓen Tinubu ya kai ƙorafin Channels TV zuwa NBC saboda tattaunawa da Ahmed Datti

Kwamitin yaƙin zaɓen Tinubu ya kai ƙorafin Channels TV zuwa NBC saboda tattaunawa da Ahmed Datti

Uncategorized
Kwamitin yaƙin zaɓen Tinubu ya kai ƙorafin Channels TV zuwa NBC saboda tattaunawa da Ahmed Datti   Kwamitin yakin neman zaɓen shugaban kasa na jam’iyyar APC ya kai ƙorafi ga hukumar yada labarai ta kasa, NBC, inda ya bukace ta da ta sanya wa Channels TV takunkumi.   A cikin koradin da ya shigar, mai dauke da kwanan watan 28 ga watan Maris da kuma mika wa babban daraktan hukumar NBC, kwamitin ya zargi mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Datti Baba-Ahmed, da yin kalamai da dama na tunzuri, wanda ke nuna rashin amincewar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na ranar 25 ga Fabrairu, 2023   Takardar koken mai dauke da sa hannun Bayo Onanuga, ta bukaci hukumar da ta kakaba wa gidan talabijin din takunkumin da ya dace.   A wani bangare...
Ramadan: Ƴansanda sun kama mutane 14 da zargin aikata fashi da dabanci a Kano 

Ramadan: Ƴansanda sun kama mutane 14 da zargin aikata fashi da dabanci a Kano 

Uncategorized
Ramadan: Ƴansanda sun kama mutane 14 da zargin aikata fashi da dabanci a Kano   Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta sanar da kama mutane 14 waɗanda ta ke zargi da aikata fashi da makami da ta'ammali da ƙwayoyi da kuma aikata dabanci a makon farko na watan azumin Ramadan.   Rundunar ta ce an samu nasarar kama mutanen ne a wani samamen da rundunarta ta dawo da zaman lafiya ta kaddamar.   Ta ce ta kuma ƙwato muggan maƙamai da haramtattun ƙwayoyi da kuma kayayyaki da aka sata.   A wata sanarwa da kakakin runduar ƴan sanda jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce kwamishinan ƴan sandan jihar, Mamman Dauda ya ayyana yaki kan duk wani nau'i na aikin dabanci a faɗin jihar.   Ƴan sandan sun ce suna iyaƙar kokarinsu wajen dakile dukkan ay...
Ba za a sa wa Trump ankwa ba idan ya je kotu in ji lauya

Ba za a sa wa Trump ankwa ba idan ya je kotu in ji lauya

Uncategorized
  Ba za a sa wa Trump ankwa ba idan ya je kotu in ji lauya   Lauyan tsohon shugaban Amurka ya ce ba za a sanya wa Donald Trump ankwa ba, idan ya halarci zaman kotu a New York a makon gobe.   An tambaye shi ne a gidan talbijin na ABC News ko yaya yake zaton tsarin gurfanar da Trump gaban kotu zai kasance, Joe Tacopina ya ce ya "tabbata [masu shigar da ƙara] za su yi ƙoƙarin samun duk wani ɗigo na jan hankalin jama'a da za su iya, a kan wannan abu.   Amma ya ƙara cewa ba za a sa wa shugaban ankwa ba".   Tun farko rahotanni sun tabbatar da Za a iya kama Donald Trump nan da ƴan kwanaki. Lauyan Trump ya ce: "Na fahimci cewa za su rufe hanyoyin zuwa yankin da ke zagaye da kotun, idan an zo gurfanar da shi, kuma su rufe ginin kotun.   ...
NADECO ta buƙaci SSS da su kamo waɗanda su ke adawa da miƙa mulki ga Tinubu

NADECO ta buƙaci SSS da su kamo waɗanda su ke adawa da miƙa mulki ga Tinubu

Uncategorized
NADECO ta buƙaci SSS da su kamo waɗanda su ke adawa da miƙa mulki ga Tinubu   Wata kungiyar rajin kare dimokradiyya ta kasa, NADECO, ta bukaci hukumar tsaro ta farin kaya, SSS, da ta damke wasu mutane da ke da niyyar kawo cikas ga mulkin dimokuradiyya na mika mulki daga shugaban kasa Muhammadu Buhari zuwa Sen. Bola Tinubu.   Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Farfesa Atilade Adeeyo ya fitar a Oye-Ekiti.   “Mu na kira ga hukumar ta DSS da ta kawo karshen ayyukan rashin demokradiyya da rashin kishin kasa da ke kokarin kawo cikas ga tsarin mulkin dimokuradiyya daga gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari zuwa ga zababben shugaban kasa.   “Al’ummar kasar nan ta shaida yadda aka gudanar da zaben shugaban kasa cikin kwanciyar ...
Kungiyar agaji ta Qatar ta tallafawa magidanta 8 da shanu 40 a Sokoto 

Kungiyar agaji ta Qatar ta tallafawa magidanta 8 da shanu 40 a Sokoto 

Uncategorized
Kungiyar agaji ta Qatar ta tallafawa magidanta 8 da shanu 40 a Sokoto   A ranar Juma’a ne kungiyar agaji ta Qatar Charity tare da hadin gwiwar hukumar zakka da bayar da tallafi ta jihar Sokoto, SOZECOM, ta kaddamar da sabon aikinta mai taken “Shirin Tallafin Shanu ga Mabukata” a jihar.   An fara bikin kaddamarwar ne da iyalai takwas daga cikin ‘yan gudun hijirar daga Gandi da ke karamar hukumar Rabah a jihar.   A nasa jawabin, Muhammad Maidoki, Shugaban SOZECOM, ya yabawa wadanda suka samar da wannan shiri.   Maidoki ya ce tsarin wani sabon salo ne wanda zai yi tasiri matuka ga rayuwar mutane da dama wajen tabbatar da dorewar al'umma.   "Ba mu da isassun kalmomi da za mu gode wa da yawa daga cikin ayyukan da Qatar Charity ta yi wa muta...