Friday, February 14
Shadow

Ba A Bi Umarnin Da Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Bayar Na Sake Fasalin Naira Ba>>Tsohon Daraktan CBN Ga Kotu

Tsohon Daraktan Ayyuka na Kudi a Babban Bankin Najeriya (CBN), Ahmed Bello Umar, ya shaida wa babbar kotun Abuja da ke Maitama cewa ba a bi umarnin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar na sake fasalin Naira ba.

Ya bayyana cewa takardar kudin Naira da aka sake gyarawa a karkashin tsohon Gwamna Godwin Emefiele sun sha bamban da bayanan da tsohon shugaban kasar ya amince da su.

Daga: Abbas Yakubu Yaura

Karanta Wannan  Tsadar rayuwa: Tsohon Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Aminu Waziri Tambuwal ya ce sai da suka yi wa 'yan Nijeriya gargadi kar su sake yin kuskuren zaben jam'iyyar APC a zaben 2023

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *