fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Bacin ran ‘yan Najariya muka guda shiyasa bamu cire tallafin mai ba>>Gwamnatin tarayya

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, bacin ran ‘yan Najariya ta guda shiyasa bata cire tallafin man fetur ba.

 

Hakan na kunshene a cikin maganar da kakakin shugaban kasa, Malam Garba Shehu yayi a ganawar da aka yi dashi a gidan talabijin na channels TV, kamar yanda the Cable ta ruwaito.

 

Yace gwamnati na duba maslahar jama’a a duk sanda zata gudanar da wani tsari dan daukar matsayin da ya dace.

 

A zamanin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan dai ya gamu da fushin ‘yan Najariya a lokacin da yayi yunkurin cire tallafin na man fetur.

 

Wanda daga baya dole tasa ya hakura da wannan aniya tasa.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *