fbpx
Saturday, March 25
Shadow

“Bazamu ki yin abinda ya kamataba dan a yabemu”>>Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru El-Rufai ya bayyana cewa gwamnatinshi bazata ki yin abinda ya kamataba kawai dan wasu su yabeta na dan wani lokaci, yace zasu yi abinda ya kamata dan magance matsalolin dake damun jama’a.


(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});

Ya kara da cewa ba zasu bi masu ganin cewa su na musammanneba, amma zasu bayar da dama wadda kowa zai iya amfana da ita, ya kara da cewa kuma yayi amannar cewa mutanen jihar sun san cewa wannan zabi da gwamnati tayi na warware matsaloli ta hanyoyi masu tsauri shine ya kamata kuma domin amfanin sune.
Gwamnatin jihar dai ta sallami wasu malaman makarantar firaimare a jihar su kimanin dubu ashirin da biyu, bayan data shirya musu wata jarabawa amma mafi yawanci basu ciba, abinda ya dauki hankulan mutane sosai, ba a jihar Kaduna kadai ba, harda, harma gaba dayan kasar, bayan nan kuma gwamnatin jihar ta sallami wasu ma’aikatan kananan hukumomi.


(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});

Karanta wannan  Zan Garzaya Kotu Domin Kalubalantar Yawan Kuri'u Da Jam'iyyar PDP Ta Samu A Zaɓen Gwamna Duk Da Nasarar Da Na Samu, Cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *