Ƙungiyar ISWAP da ke iƙirarin jihadi a Yammacin Afrika ta ɗauki nauyin kai hari gidan yarin Kuje da ke babban birnin tarayyar Najeriya Abuja.
A wani saƙo da ƙungiyar ta wallafa a wani shafin intanet da ƙungiyar ta saba yaɗa farfaganda, ƙungiyar ta ce ta saki fursunoni da dama.
VIDEO: ISWAP Terrorists Release Footage Claiming Responsibility For Kuje Prison Attack https://t.co/NhGrLVgJCQ
In a video clip on Wednesday night, the terrorist group showed some of its men shooting their way into the custodial center. pic.twitter.com/UG27z1sdNg
— LEADERSHIP NEWS (@LeadershipNGA) July 6, 2022
Hukumomin Najeriya dai sun ce akwai fursunoni sama da 400 da har yanzu ba a gansu ba tun bayan harin da aka kai gidan yarin.