fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Bidiyon yanda magidanci ya kama matarsa da kwarata da take soyayya dasu a kafafen sada zumunta

Babban Malamin Addinin Islama, Sheikh Aminu Ibrahim Daurarawa ya bayyana yanda suka samu wani labari mara dadi tsakanin wasu ma’aurata.

 

Malam ya bayyana a wani wa’azi da yayi cewa, wata matace mijinta ya kamata tana soyayya da mazaje daban-daban a shafukan sada zumunta.

 

Bayan da ya kamata, sai ta amince ta yi laifi ta bashi hakuri kuma aka ci gaba da zama, saidai daga baya an bashi shawarar ya sayi layin da bata sani ba ya mata magana dan tabbatar da ta daina.

 

Ya kuwa aikata hakan kuma sai ta ci gaba inda taita zagin mijin mata da fadar halayensa marasa kyau.

Karanta wannan  Mun nunawa Abba Gida-Gida Soyayya amma ya nuna mana kiyayya>>Inji Wani da aka rushewa shago a Kano

 

Ya gaya mata cewa da zata yadda mijinta ya saketa, zai aureta, nan kuwa tace ta amince, ta je ta fara yiwa mijinta balbalin bala’i cewa sai ya saketa.

 

Dan jin cikakken labarin danna nan ku kalli bidiyon

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *