Da Dumi Duminsa: Binani ta janye karar data shigar kan hukumar zabe.
'Yar takarar gwamnan jihar Adamawa karkashin tutar APC, Aisha Binani ta janye karar data shigar akan hukumar zabe ta kasa,INEC.
Binani ta shigar da karar kan cewa ita ce tayi nasara domin kwamishinan hukumar zaben, Hudu Yunusa Ari ya bayyana hakan.
Amma yanzu ta janye wannan kara data shigar, bayan gwamna Fintiri yayi nasarar lashe zaben jihar.
Yanzu Yanzu shugaban kasa Muhammadu Buhari ya rantsar da sakatarori guda shiga na dindindin yayin dayake shirin barin ofishi.
A ranarv29 dai shugaban kasar zai bar ofishi ya mikawa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu mai jiran gado.
Yanzu Yanzu 'yan bindiga sunyi garkuwa da shugabar kidaya (Census) sun bukaci naira miliyan 500.
Yan bindigar sunyi garkuwa da shugabar kidayar ta jigar Bayelsa ne, Gloria kamar yadda hukumar 'yan sandae jihar ta bayyana.
Sunyi garkuwa da ita ne a ranar lahadi kuma sun bukaci kudin famsa naira miliyan 500.
Malama Glori dai ta kasance tsohuwar shugabar ma'aikata na jihar Bayelsa, kuma anyi garkuwa da ita ne tare da masu tsaron ta.
Wata Sabuwa: 'Yan Najeriya sun shiga rudani bayan ganin wani abu a hammatar zababben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
A tau zababben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo guda Najeriya bayan ya shafe kusan wata guda a kasar Faransa.
Membobin jam'iyyar APC sun tarbe shi a tashar jirgi wanda ana ne aka ga wani sabon abu a hammatarsa wanda ba a san dashi ba.
Dama akwai wasu 'yan kasar dake cewa bashi da cikakkiyar lafiya.
9 News Nigeria.
Hotuna: Wani jirgi saman Amurka ya kama da wuta a sararin samaniya
Tuni matukin jirgin ya dawo filin ya sakko da fasinjojin dake cikin jirgin.
Ya kama da wutar ne bayan mintuna 40 da tashin sa.
Wata 'yar matsala ce jirgin ke fama.dashi amma ba inji bane kamar yadda rahotanni suka bayyana.
YANZU-YANZU; Gwamnatin Najeriya ta bukaci Daliban Najeriya mazauna kasar Sudan da su zauna a inda suke kar su tsallake zuwa Kan iyakoki.
Haka zalika Malam Garba shehu ya bayyana cewa basu dauki Alkawarin kwashe duk Yan Najeriya gaba daya ba. Saboda akwai yan asalin Najeriya haifaffun chan.
A Cewar Malam Garba Shehu yayin ganawarsa da Gidan Radio na BBC Hausa.
Yanzu Yanzu shugaban kamfanin sufurin jirgin sama na Air Peace, Onyema ya dauke nauyib dawo da 'yan Najeriya da suka makale a yakin Sudan kyauta.
Onyema yace zai taimaka ne domin Allah saboda Najeriya ba zata laminci rasa 'yan kasarta haka nan ba.
Yace muddin zasu yi kokarin shiga wata kasar dake kuda da su to tabbas zai dauko su ya dawo dasu Najeriya.
Domin yanzu jirgin waje baya tashi a Sudan saboda rikicin da akeyi a kasar.
Yace ba komai ne za a riga dorawa a wuyan gwamnati ba musamman irin wannan bukatar ta gaggawa.
Bidiyo: Kiris ya rage wani Davido yasha naushi a wurin wani dan kallo yayin da yake wasa a Legas.
https://twitter.com/MobilePunch/status/1650400497998675969?t=jSyiF9C64CI9Nv74y4WARw&s=19
Bidiyo: Kiris ya rage wani Davido yasha naushi a wurin wani dan kallo yayin da yake wasa a Legas
Tsohon Kwamishinan ayyuka na jihar Kano, Engr. Mu’azu Magaji Dan-Sarauniya (Win-Win), ya furta wani kalami game da neman afuwa da shuganni da wa’adin mulkinsu ya zo ƙarshe ke yi a baya -bayan nan ke yi na neman afuwar al’ummar su.
A baya-bayan nan ne aka jiyo shugaban ƙasa Muhammadu Buhari yana cewa, yana neman alummar Nigeria su yafe masa idan har yayi musu wani abu marar kyau bisa kuskure.
Haka zalika shima Gwamnan jihar Kano mai barin gado, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya furta irin wannan kalami na neman afuwar alummar da ya mulka.
Tsohon Kwamishinan na jihar Kano ya bayyana hakan ne ta cikin hakan ne ta cikin wani sako da ya wallafa shafinsa na Facebook.
Inda ya ce, “Wato Ina jinjina yafewa G...