
Da Dumi Dumi: Yan ta’adda sun kaiwa jirgin kasan yakin neman zaben gwamnan jihar Osun hari
Wasu 'yan ta'adda da ake kyautata zaton 'yan bangar siyasa ne sun kaiwa jirgin kasan yakin neman zaben gwamnan Osun hari watau, Adegboyega Oyetola.
'Yan ta'addan sun kai harin ne a ranar litinin kuma a ciki hadda motar manema labarai ta NUJ wadda itama suka lalata ta.
Kuma sun jiwa wasu manema labarai rauni. A takaice dai sun lalata motoci kusan goma a harin da suka kaiwa gwamnan.