Sunday, January 19
Shadow

Duk Labarai

Wata sabuwar Kungiya me cike da hadari da bata yadda da kowane irin addini ba ta bayyana a Kaduna

Wata sabuwar Kungiya me cike da hadari da bata yadda da kowane irin addini ba ta bayyana a Kaduna

Duk Labarai
Hukumar kula da shige da fici a Najeriya, NIS ta bayyana samuwar wata kungiya me suna ACHAD a jihar Kaduna. Rahotanni sun bayyana cewa Kungiyar na neman mabiya kuma bata yadda da wani addinin Musulunci ko na Kiristanci ba. Hakanan an bayyana cewa kungiyar na safarar mutane musamman kananan yara. An jawo hankalin mutane da su gaggauta sanar da hukumomi da zarar sun ga abinda basu ganemawa ba.
Matashi ya sha duka, yana fuskantar barazanar kkisa saboda yana yawan kunna wakokin Rarara

Matashi ya sha duka, yana fuskantar barazanar kkisa saboda yana yawan kunna wakokin Rarara

Duk Labarai
Bayan Ya Šha Dukan Tsiya Akan Yawan Kunna Wakokin Rarara, Yanzu Kuma An Soma Ýi Màsa Baŕazanaŕ Ķìšà Matashi Atiku dan jihar Kano na fuskantar barazana sakamakon kwashe tsawon lokaci da ya yi yana nuna soyayya tare da kunna wakokin Mawaki Rarara a shagonsa, lamarin da ya jawo masa dukan tsiya daga wasu matasan Unguwa. Rahotanni na cewa yanzu haka wannan matashin ya gagara zuwa shagon sa inda gudanar da kasuwancin sa sakamakon barazanar da ýake fuskantar daga wasu matasa. Yanzu haka dai matashin na shan magunguna tun bayan lokacin da aka lakada masa duka domin ya samu rauni da dama a jikinsa.
Umma Shehu tasa an kama shehun Tiktok saboda kazafın zina

Umma Shehu tasa an kama shehun Tiktok saboda kazafın zina

Duk Labarai
Umma shehu tasa an kama shehun tiktok saboda kazafın zina {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A kwanakin baya ne Shehun Tiktok yai wani Video inda ya ambaci sunan Umma Shehu tare da kafe hoton ta yace itace take daurewa zina gindi ake yinsa ko yaushe. Kalaman nasa sunyi tsauri wanda yasa ta ɗauki matakin gaggawa kuma ta bayyana cewa ba zata yafe masa ba har sai an ƙwata mata hakkin ta. Ga bidiyon nasa: Dannanan da Kallo https://www.tiktok.com/@suba_neh/video/7457878476910087430?_t=ZM-8tBvk6AoQ5O&_r=1 ...
Wata Sabuwa: Ana Rade-Radin Gwamnatin Tinubu ta tursasa tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari zuwa kotu, saidai gwamnatin tace maganar sirri ce

Wata Sabuwa: Ana Rade-Radin Gwamnatin Tinubu ta tursasa tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari zuwa kotu, saidai gwamnatin tace maganar sirri ce

Duk Labarai
Wasu rade-radi sun bayyana a kafafen sada zumunta cewa gwamnatin tarayya ta bukaci tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya je wata kotu a kasar Faransa yayi bayani. An shigar da wata karane kan aikin tashar wutar lantarki ta Mambila inda ake neman Dala Biliyan $6. Saidai a martanin da me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuna ya fitar yace wannan magana ba haka take ba. Ya tabbatar da cewa, an shigar da kara wanda ake yinsa a sirri kuma duka manyan mutanen da suka je suka yi bayani a wajan kotun, sun yi hakanne bisa radin kansu da kuma nuna kishin kasa amma ba gwamnatin tarayya ce ta tursasasu ba. Ya kara da cewa, ko kadan bai kamata ace an wallafa labarin shari'ar ba saboda ta sirri ce har sai kotu ta kammala bincikenta. Saidai yace gwamnatin na godiya ga duka wadand...
Banson kasata Ingila ta zama kamar matalauciyar kasa Najeriya>>Inji Kemi Badenoch

Banson kasata Ingila ta zama kamar matalauciyar kasa Najeriya>>Inji Kemi Badenoch

Duk Labarai
Shugabar Jam'iyyar 'yan ra'ayin mazan jiya ta kasar Ingila, UK Conservative Party, Kemi Badenoch ta sake sukar 'yan Najeriya duk da cewa ita 'yar asalin Najeriyar ce. Da take magana ta farko a shekarar 2025 a wajan wani taro na musamman ranar Alhamis, Kemi tace bata son ingila ta zama kamar Najeriya, tace ta ga yanda danginta masu hali suka tsiyace saboda rashin gwamnati me kyau da tsadar rayuwa da ta yi yawa. Kemi na 'yar shekaru 16 ta bar Najeriya zuwa kasar Ingila da kudin babanta na karshe wanda basu wuce fan £100 ba. Kemi ta kara da cewa, tana aiki tukuru domin ganin wahalar da ke Najeriya bata maimaitu a kasar Ingila ba. A baya, Kemi ta zagi 'yan Najeriya da cewa 'yan fashi da makami ne.
Kuma Dai: Kalli Bidiyon tsìraìcì na wata ‘yar Tiktok ya bayyana

Kuma Dai: Kalli Bidiyon tsìraìcì na wata ‘yar Tiktok ya bayyana

Duk Labarai
A yayin da a baya bidiyin tsiraici na 'yan Tiktok yayi tashen bayyana, an samu saukin lamarin. A baya dai bidiyon 'yan Tiktok irin su Babiana, Hafsat Baby da sauransu ya bayyana wanda ya dauki hankula a kafafen sada zumunta. A yanzu ma na wata da ake cewa Shalelene ya bayyana. Shalele dai ta yi suna wajan sukar mutane da yawa a shafin nata na TikTok wanda hakan ne yasa wasu ke kurnar ganin bidiyon ta itama ya bayyana. https://www.tiktok.com/@juniorsadeq7/video/7460639878242405637?_t=ZM-8t8dRHhXZRd&_r=1 Kazancewar Bidiyon ya nuna tsiraici da yawa ne yasa shafin hutudole.com ba zai iya wallafashi ba.
Ana zargin shugaban bankin First Bank da satar Naira Biliyan 12.3

Ana zargin shugaban bankin First Bank da satar Naira Biliyan 12.3

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa hukumar yaki a rashawa da cin hanci, EFCC zata gurfanar da tsohon shugaban bankin First Bank Stephen Onasanya a gaban kotu bisa zargin satar Naira Biliyan 12.3. Babbar kotun tarayya dake Legas ta saka ranar 20 ga watan Janairu dan fara sauraren karar da EFCC ke yi akan Onasanya da shugaban kamfanin Flourmills Group, Oba Otudeko. Akwai kuma Soji Akintayo wanda shima yana cikin wadanda ake zargi da kuma wani kamfani me suna Anchorage Leisure wanda duka ake zargin sun hada hannu wajan yin wannan sata.  Ana zargin sun aikata satarne a tsakanin shekarun 2013 zuwa 2014.
Gwamnatin Tarayya ta ware N252.89bn dan ci gaba da gyaran titin Abuja zuwa Kano tace cikin watanni 12 za’a kammalashi

Gwamnatin Tarayya ta ware N252.89bn dan ci gaba da gyaran titin Abuja zuwa Kano tace cikin watanni 12 za’a kammalashi

Duk Labarai
Gwamnatin ta sanar da amincewa da fitar da Naira N252.89bn dan ci gaba da gyaran titin Abuja zuwa Kano. Ministan Ayyuka, Dave Umahi ne ya tabbatar da hakan inda yace za'a gabatar da wannan magana a gaban majalisar zartaswa ta kasa dan amincewa da ita. Kamfanin da aka baiwa kwangilar wannan aiki shine Infoust Nigeria Limited. Ministan yace za'a yi amfani da fasahar zamani dan gyaran titin wanda ke saukaka tafiye-tafiye da cinikayya tsakanin kudu da Arewa.
Bankin Duniya yace Tattalin arzikin Najeriya zai karu da kaso 3.6

Bankin Duniya yace Tattalin arzikin Najeriya zai karu da kaso 3.6

Duk Labarai
Bankin Duniya ya bayyana cewa, tattalin arzikin Najeriya zai karu da kaso 3.6 tsakanin shekarar 2025 zuwa 2026. Bankin yace hakan zai farune bayan da Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta dauki matakan tada komadar tattalin arziki. Bankin yace bangarorin da suka fi samun tagomashi sune na kudi da kuma sadarwa. Matakan da gwamatin Shugaba Bola Ahmad Tinubu ta dauka sun hada da cire tallafin man fetur da karya darajar Naira da sauransu.
Wahalar rayuwa a Najeriya tasa mata sun fara aikin Jari Bola

Wahalar rayuwa a Najeriya tasa mata sun fara aikin Jari Bola

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wahalar rayuwa a Najeriya tasa mata sun fara aikin jari Bola wanda aiki ne da aka fi sanin maza da yi. An ga matan na aikin Jari Bola ne a Jihar Legas inda jaridar Vanguard tace yawancinsu matan aurene. Wasu daga cikin matan da jaridar ta yi hira dasu sun bayyana cewa, Mazajensu ne suka rasu wasu kuma sun bayyana cewa an kori mazajensu daga wajan aiki ne da dai sauran matsalolin rayuwa. Tun bayan hawan mulkin Shugaba Bola Ahmad Tinubu kuma ya cire tallafin man fetur a ranar farko da ya karbi mulkin, kasar ta fada cikin matsin tattalin arziki wanda har yanzu ba'a warware ba.