Da Duminsa: Adam A. Zango ya kara aure
Rahotanni sun bayyana cewa Tauraron fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya kara aure kwanaki kadan bayan rabuwa da tsohuwar matarsa, Maimuna.
Wadda ya aura, Maryam Gombe ce ta wallafa labarin inda tace a yau an daura mata aure da baba Ado.
Maryam tace duk wanda tawa laifi tana fatan ya yafe mata kuma tana fatan Allah ya basu zaman Lafiya.
Hutudole ya dade da lura da cewa akwai soyayya tsakanin Adam A. Zango da Maryam.
Domin a baya ta sassaka Hotuna da Bidiyon su tare.
Maryam Dai ittace wadda Ordinary President Ahmad Isa yaso kaita kotu kara saboda zargin bata suna








