fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Kasuwanci

Akwai yiyuwar kara farashi man fetur a Najeriya

Akwai yiyuwar kara farashi man fetur a Najeriya

Kasuwanci
Rahotanni sun nuna cewa akwai yiyuwar gwamnatin Najeriya ta kara farashin kudin da ake sayar da litar Man Fetur a kasar.   Hakan ya bayyana a filine bayan karuwar farashin gangar danyen man fetur a kasuwar Duniya zuwa Dala 35. A baya dai hukumar dake kula da kayyade farashin Man a Najeriya, PPPRA ta rage farashin man zuwa 125 bayan faduwar da yayi a kasuwannin Duniya.   A karo na 2 ma ta sake rasge farashin man zuwa 123.5 bayan kara faduwa da farashin man yayi zuwa kasa da Dala 30 a kasuwannin Duniya.   Saidai hukumar ta bayyana cewa farashin da ake sayar da man a Najeriya zai rika sauka da tashine bisa la'akari da farashin man a kasuwannin Duniya.   Hakan yasa wani daga cikin mahukuntan wanda baya so a bayyana sunansa ya gayawa Punch cewa...
Kayan Masarufi sun yi tashin gwauron zabin da ba’a taba gani ba cikin kusan shekaru 2>>NBS

Kayan Masarufi sun yi tashin gwauron zabin da ba’a taba gani ba cikin kusan shekaru 2>>NBS

Kasuwanci
Hukumar Kididdiga ta kasa,NBS ta fitar da kididdigar hauhawan farashin kayan Masarufi na watan Afrilun daya gabata.   Sakamakok kididdigar ya nuna cewa an samu tashin kayan Masarufin da kaso 12.34 wanda hakan ya nuna an samu karin kaso 0.08 idan aka kwatanta da watan Maris da aka samu kaso 12.26.   Tashin farashin kayan masarufin shine irinsa na farko cikin watanni 23 da suka gabata
Gwamnatin tarayya ta roki ‘yan kasuwa da kada su kara farashin kayan masarufi

Gwamnatin tarayya ta roki ‘yan kasuwa da kada su kara farashin kayan masarufi

Kasuwanci
Gwamnatin tarayya tayi kira ga yan kasuwa dasu guji hauhawar farashin kayayyakin abinci da sufuri yayin da kasar ke gwagwarmayar shawo kan cutar Coronavirus (COVID-19) a kasar. Alhaji Lai Mohammed, Ministan Yada Labarai, Al’adu, da yawon shakatawa ne, ya yi wannan kiran a gaban Kwamitin yaki da cutar coronavirus, a ranar Alhamis, a Abuja. Lai Ya kara da cewa akwai bukatar nuna tausayi ga dukkan ‘yan Najeriya ta hanyar sassautawa tare da hana hauhawar farashin kayan masa rufi. A cewar sa “Wannan lokaci ne da mutane ke bayar da tallafi don rage radadi ga al'umma. Inda ya kara da cewa "Muna kira ga 'yan uwanmu da kar suyi amfani da wannan damar don zaluntar jama'a.   Idan zaku iya tunawa a makwannin baya gwamnatin Jihar kano ta zauna da 'yan kasuwar jihar don cimma matsaya...
Gwamnatin Najeriya tayi barazanar daure duk wanda ke sayar da taki sama da farashin data amince dashi N5000

Gwamnatin Najeriya tayi barazanar daure duk wanda ke sayar da taki sama da farashin data amince dashi N5000

Kasuwanci
Gwamnatin Tarayya ta bukaci ‘yan Najeriya da su kai rahoton duk wani da aka samu yana sayar da takin zamani sama da farashin da Gwamnatin ta amince da shi. Shugaban Kwamitin kan takin zamani kuma gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai karin haske kan kokarin da gwamnati take wajan samar da taki mai araha ga manoma. Manema labarai sun ruwaito cewa Gwamnatin Tarayya ta rage farashin buhun taki daga dubu N5,500 zuwa dubu N5000 don tallafawa manoma, a sakamakon bullar cutar Covid-19. Shugaban kwamnitin ya kara da cewa  Gwamnatin Tarayya ta sami labarin kokarin da wasu mutane ke yi wajen dakile kokarin da gwamnati ke yi na samar da takin zamani don wadatar da manoma a Najeriya. “Mun samu labarin cewa wasu mutane suna si...
‘Yan Najeriya sun aike da sakonni sama da biliyan 1 a wata guda tunbayan gabatar da tsarin tura sako kyauta >>> MTN

‘Yan Najeriya sun aike da sakonni sama da biliyan 1 a wata guda tunbayan gabatar da tsarin tura sako kyauta >>> MTN

Kasuwanci
Kamfanin MTN Nigeria ya tattara sakonnin da aka tura ta hanyar tsarin da ya bada dama na aike sakonni kyauta har sama da biliyan 1 a Najeriya. Rahoton da Q1 na MTN ya nuna cewa sama da biliyan daya ne masu aika sakonnin suka aika a cikin makonni hudun farko na fara gabatar da sakonnin SMS kyauta wanda kamfanin ke bada damar aika sako 10 a kowacce rana har zuwa adadin 300  a kowane wata. Tsarin wanda kamfanin MTN ya gabatar ya bayyana cewa sama da mutum miliyan 70 da sukai rijista nada damar aike sakon karta kwana kyauta har 300 a wata. Wannan wani ɓangare ne na 'Y'ello Hope Package' wanda aka tsara don baiwa 'yan kasa damar aike sako a sakamakon bullar cutar coronavirus, wanda hakan zai taimaka wajan Isar da sakonni don dakile yaduwar cutar Covid-19. Idan zaku iya tunawa a ma...
Yanda ‘yan kasuwar Kantin Kwari, Wambai suka zillewa dokar hana zirga-zirga suka bude sabuwar Kasuwa a Kano

Yanda ‘yan kasuwar Kantin Kwari, Wambai suka zillewa dokar hana zirga-zirga suka bude sabuwar Kasuwa a Kano

Kasuwanci
Dokar hana zirga-zirga ta sa an kulle kasuwanni a mafi yawan jihohin Najeriya wanda ba a Najeriya ne kadai lamarin ke faruwa ba dalilin cutar Coronavirus/COVID-19.   A jihar Kano ma haka lamarin yake saidai kulle kasuwar yasa wasu da dama na tsitsi ganin cewa kasuwanci na da karfi a cikin Kano.   A lokacin da gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sassauta dokar hana zirga-zirga a ranar 2 ga watan Mayu yace an yi hakanne dan baiwa mutane dama su dayi kayan Abinci dan Watan Ramadana.   Sanarwar ta kara da cewa kayan Abinci da mayanka kawai za'a sayar sannan dole a saka abin Rufe hanci da baki dan dakile yaduwar cutar da kuma kula da tsafta, sannan a rika nesa-nesa da juna.   Saidai ba hakan ke faruwa ba a sabuwar Kasuwar da 'yan kasuwar ...
Kotu ta umarci kamfanin jirgin sama da ya biya fasinja Naira miliyan 10 kan jinkirin tashi

Kotu ta umarci kamfanin jirgin sama da ya biya fasinja Naira miliyan 10 kan jinkirin tashi

Kasuwanci
Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja (FCT) a ranar Laraba ta umarci kamfanin jirgi na Arik Air ya biya kimanin naira miliyan 10 ga wani fasinja a sakamakon jin kirin tashi da jirgin yayi wanda ya jawa fasinja tsaiko. Wani fasinja, mai suna Isa Modibbo, wanda ke da cutar ciwan sukari , ya ba da rahoton rasa ganawar sa da likitansa dake zaune a sokoto wanda aka tsara tashin jirgin daga Abuja zuwa sokoto da misalin 10: 30 na safe amma sai jirgin ya tashi da misalin karfe 6 na yamma. a ranar 16 ga watan Disamba  2017. Rashin gamsuwa da matakin kamfanin jirgin  ne yasa Modibbo shigar da kamfanin jirgin saman kara saboda “tauye hakkinsa na dan adam da aikai". Da yake yanke hukunci a ranar Laraba, Mai shari'a Danlami Senchi ya ce gazawar kamfanin sufurin jirgin sama na kin cika sharudd...
Rage kudin mai: Gwamnati na so ta hadamu fada da ‘yan Najeriya>>Masu Gidajen Man Fetur

Rage kudin mai: Gwamnati na so ta hadamu fada da ‘yan Najeriya>>Masu Gidajen Man Fetur

Kasuwanci
Kungiyar masu gidajen sayar da man fetur ta Najeriya PETROAN ta joka kan abinda gwamnati ta yi na rage kudin da take basu mai amma bata sanae da kudin da za'a rika sayar da man ba a gidajen man.   Gwamnati ta hannun kamfanin mai na kasa, NNPC wanda shine babban me shigo da mai kasarnan ta bayyana ragin kudin da take baiwa masu gidajen mai daga 113.28 zuwa 108. Saidai bata bayyana nawa za'a rika sayar da man a gidajen mai ba.   NNPC ba itace ke da alhakin bayyana kudin farashin sayar da mai a gidajen mai ba, PPPRA ce ke da wannan alhakin. Kuma duk da cewa ta yi alkawarin rika bayar da farashin mai a kowane wata amma gashi an yi nisa a watan Mayu, batace uffan ba.   Hakan yasa shugaban kungiyar ta PETROAN, Billy Gillis-Harry ya bayyana cewa gwamnatin na s...
Gwamnatin tarayya ta ware Naira biliyan 50 domin farfado da masana’antun

Gwamnatin tarayya ta ware Naira biliyan 50 domin farfado da masana’antun

Kasuwanci
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ware Naira biliyan 50 domin farfado da masana'antun kasar, bayan da suka samu koma baya sakamakon annobar cutar coronavirus.   Najeriya kasa ce mai cike da dumbin arzikin kasa. Sai dai annobar coronavirus da ta mamaye duniya ta shafi wannan fanni, wanda hakan ya tilastawa gwamnati daukar matakin da ya dace. Gwamnatin dai ta shirya domin bayar da tallafi da ya kama daga kan Naira miliyan uku zuwa 25 ga masana'antun kasar. Shi kuwa darakta janar na kungiyar masu masana'antu na kasar Mr Ambrose Uche ya koka ne kan yadda ake samun karin kudin ruwa a bankunan kasuwancin kasar.
Gwamnatin jihar Bauchi ta cimma matsaya da ‘yan kasuwar jihar don saukaka kayan masarufi inda Buhun shinkafa zai koma 17,500

Gwamnatin jihar Bauchi ta cimma matsaya da ‘yan kasuwar jihar don saukaka kayan masarufi inda Buhun shinkafa zai koma 17,500

Kasuwanci
Yan kasuwa a Bauchi sun amince za suna sayar da shinkafa akan dubu 17,500 Gwamnatin jihar Bauchi ta cimma matsaya da 'yan kasuwar jihar kan sassauta farashin kayan masarufi bisa halin da al'umma suke ciki. A Cikin wata sanarwa da Gwamnatin jihar Bauchi ta fitar da sa hannu  mataimakin gwamnan jihar kan yada labarai Mukhtar Gidado a cewar sa an yi zama na musamman tsakanin kwamnitin yaki da cutar Covid-19, da kuma bangarorin 'yan kasuwar jihar inda aka cimma matsayar  sassauta farashin kayan masarufi. Kayayya kin da aka cimma matsaya akan sa sune shinkafa wanada za'a na siyarwa akan Naira dubu 17,500. Sai kuma sukari inda za'a na siyarwa akan 17,000. Sai kuma gero akan Naira 12,500. Manja Naira 9,000 Sai nama kilo daya kuma 1,200.