fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Kiwon Lafiya

Coronavirus/COVID-19: Shugaban ‘yansandan Najeriya ya bukaci a rage zuwa ofishin ‘yansanda in ba dole ba sannan ‘ya sandan su rage kama mutane

Coronavirus/COVID-19: Shugaban ‘yansandan Najeriya ya bukaci a rage zuwa ofishin ‘yansanda in ba dole ba sannan ‘ya sandan su rage kama mutane

Kiwon Lafiya
Shugaban 'yansandan Najeriya,Muhammad Adamu ya  bukaci 'yan Najeriya da su rage zuwa ofishin 'yansanda in ba wai abin ya zama dole ba.     Ya fitar da sanarwarne ta hannun me magana da yawun rundunar,Frank Mba inda yace suma 'yan sanda su kula da lafiyar jikinsu kan yanda ake fama da cutarnan na Coronavirus/COVID-19.   Ya bukaci 'yansandan da kansu rage kamawa da tsare mutane indai ba abinda ya shafi ta'addanci ko fashi da makami ko kisa da sauran laifikan da ba'a bayar da beli akansu ba.   Ya bukaci bincike da tantance masu laifi kamin a tsaresu.   Sanarwar ta kara da cewa, 'yansanda su ta batar su  tsaida dokar hana taruwar mutane da gwamnatin tarayya ta saka a yankunan da suke aiki.   Sanna kuma a kulle makarantun horar da '...
Mutane 532 ne suka kamu da cutar Coronavirus/COVID-19 a kasashen Iran da Sifaniya a yau

Mutane 532 ne suka kamu da cutar Coronavirus/COVID-19 a kasashen Iran da Sifaniya a yau

Kiwon Lafiya
Rahotanni daga kasar Iran, daya daga cikin kasashen da Cutar Coronavirus/COVID-19 ta yi kamari ta bayyana cewa mutane 129 ne suka mutu a yau, Lahadi.   Hakan ya kai yawan mutanen da suka mutu a kasar zuwa 1,685. Me hulda da jama'a na ma'aikatar lafiya ta kasar, Kianouche Jahanpour ya bayyanawa manema labarai cewa an samu karin mutane  da suka kamu da cutar 1,028 wanda ya kai yawan wanda suka kamu a kasar zuwa 21,638.   A kasar Sifaniya ma Kanfanin dillancin Labarai na AFP ya bayyana cewa mutane 394 ne suka mutu a ra a daya.  
Coronavirus/COVID-19: Muma mun dakata da aiki sai yanda hali yayi>>Kungiyar Karuwai ta Najeriya

Coronavirus/COVID-19: Muma mun dakata da aiki sai yanda hali yayi>>Kungiyar Karuwai ta Najeriya

Kiwon Lafiya
Kungiyar karuwai ta kasa, NANP ta bayyana cewa ita ma dai ta bi sahu wajan dakatar da kwanciya da maza har sai yanda hali yayi saboda cutar Coronavirus/COVID-19.   Shugabar kungiyar, Tamar Tion ce ta bayyanawa Manema labarai na Daily Trust haka inda tace suna umartar duk membobinsu da su dakata da aiki sai yanda hali yayi.   Ta kara da cewa karuwan su kuma daina zuwa gidan rawa dan amfanin kansu. Ta basu shawarar rika wanke hannu da kaucewa shiga taron jama'a.  
Taufa! An killace shugabar Jamus, Angela Merkel Saboda Coronavirus/COVID-19

Taufa! An killace shugabar Jamus, Angela Merkel Saboda Coronavirus/COVID-19

Kiwon Lafiya
Labarin dake fitowa daga kasar Jamus na cewa an killace shugabar kasar, Angela Merkel saboda fargabar cewa ta kamu da cutar Coronavirus/COVID-19.   An killace Merkel ne bayan da aka samu wani likita daya dubata da cutar. An bayyanawa shugabar halin da ake cikine jim kadan bayan da ta wa 'yan kasarta jawabin cewa an hana taron mutane fiye da 2.   Me magana da yawun shugabar, Steffen Seibert ya bayyana cewa shugabar zata ci gaba da aiki daga gida. Amma yayi wuri a yanke hukunci kan matsayin da ake ciki.
CRONAVIRUS: Gwamnan Jigawa Ya Bada Umarnin Rufe Makarantu A Jihar

CRONAVIRUS: Gwamnan Jigawa Ya Bada Umarnin Rufe Makarantu A Jihar

Kiwon Lafiya
Gwamnan jihar Jigawa Muhammad Badaru ya bada umarnin rufe makarantun firamare da na Sakandare dake jihar a sakamakon barazanar cutar Coronavirus.     Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dr Lawan Yunusa Danzomo ne ya bayyana hakan, inda ya ce Gwamna Badaru ya bada umarnin rufe duk wata makarantar firamare da ta sakandare dake fadin jihar.     Yace daukar matakin ya zama wajibi saboda bullar cutar a Nijeriya da wasu kasashen duniya.     Kwamishin ya bukaci iyayen yara da su debo yaransu daga makarantun daga jiya Asabar zuwa yau din nan.     Kwamishin ya ce za a rufe makarantun ne daga gobe Litinin 23 ga wannan watan.
Yanzu-Yanzu:An samu karin mutum 3 dauke da Coronavirus/COVID-19 Najeriya

Yanzu-Yanzu:An samu karin mutum 3 dauke da Coronavirus/COVID-19 Najeriya

Kiwon Lafiya
Rahotanni daga jihar Legas na cewa an samu karin mutane 3 da suka kamu da Annobar cutar Coronavirus/COVID-19 a yau, Lahadi.   2 daga cikin wanda suka kamu din sun dawo ne daga kasar waje, sai kuma mutum dayan wanda yayi ma'amala dasu ne. https://twitter.com/NCDCgov/status/1241768200653672452?s=19 Yawan wadanda ke dauke da cutar a Najeriya yanzu ya kai mutane 30 kenan
Sama da mutum 300,000 na dauke da cutar Covid-19 a Duniya

Sama da mutum 300,000 na dauke da cutar Covid-19 a Duniya

Kiwon Lafiya
A karshen makon nan, rahotanni sun tabbatar da cewa sama da mutum 300,000 sun kamu da coronavirus a fadin duniya, a nahiyar Afrika kuma sama da mutum dubu daya. Kasar Italiya ce kan gaba a yawan masu dauke da wannan annoba a fadin duniya da mutum sama da dubu 50. Sama da mutum 4,800 ne suka mutu sakamakon wannan cuta a kasar ta Italiya. Hukumar da ke kula da yaduwar cututtuka a nahiyar Afirka ta bayyana cewa mutum 108 sun warke daga cutar. Sai dai ana ta samun bullar annobar daya bayan daya a kasashen na Afirka inda yawan masu dauke da cutar ke karuwa.
Yanzu-Yanzu:Gwamnatin Kano ta rufe makarantun Islamiya saboda Coronavirus/COVID-19

Yanzu-Yanzu:Gwamnatin Kano ta rufe makarantun Islamiya saboda Coronavirus/COVID-19

Kiwon Lafiya
Gwamnatin jihar Kano ta dauki matakin rufe makarantu Islamiya dan kaucewa yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19.   Hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad ya tabbatar da haka ta shafinsa na sada zumuntar Twitter. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/1241752193826533377?s=19 Matakin na zuwane bayan gwamnatocin jihohin Najeriya suka kulle makarantu da hana taruwar jama'a.