fbpx
Saturday, September 23
Shadow

labaran duniya na yau

Likitocin Uganda sun roƙi Yoweri Musaveni ya tsaya takarar shugaban ƙasar a karo na bakwai

Likitocin Uganda sun roƙi Yoweri Musaveni ya tsaya takarar shugaban ƙasar a karo na bakwai

labaran duniya na yau
Wasu gungun likitoci a Uganda sun haifar da cece-ku-ce bayan da suka durƙusa a gaban shugaban ƙasar Yoweri Musaveni suna roƙon sa ya tsaya takarar shugaban ƙasa a karo na bakwai. Musaveni mai shekara 78 ya kasance kan mulki tun shekarar 1986. Sannan za a gudanar da zaɓen ƙasar na gaba ne a shekarar 2026. Likitocin ƙarƙashin Ƙungiyar likitoci ta Uganda (UMA) suna halartar wani taro ne kan kishin ƙasa a Kampala, babban birnin ƙasar, lokacin da shugabansu ya jagorance su suka duka a gaban shugaban ƙasar domin roƙon sa. Shafin yaɗa labaru na Nile Post ya ruwaito shugaban ƙungiyar likitocin Dr Samuel Odongo Oledo na yaba wa shugaban ƙasar, wanda ya ce ya gyara harakar kiwon lafiya tare da inganta walwalar likitoci. Daga BBChausa.
Wata mata a Amurka ta yi kokarin bude kofar jirgin sama ana tsaka da tafiya

Wata mata a Amurka ta yi kokarin bude kofar jirgin sama ana tsaka da tafiya

labaran duniya na yau, labarin jahar sokoto a yau
Wata mata ta yi kokarin tilasta wa jami’an jirgin Southwest Airlines da ya tashi daga Houston zuwa Columbus, da Ohio yin saukar gaggawa a Little Rock, Arkansas a ranar Asabar din da ta gabata, bayan da ta yi ikirarin cewa Yesu ne ya bata umarnin ta bude kofar jirgin.   Bayanan da kotun Arkansas sun ce matar mai shekaru 34 ta nufi kujerar baya a cikin jirgin, inda ta rika kallon kofar da ake amfani da ita wajen fitar gaggawa. A cewar kotun, guda daga cikin jami’an jirgin ya shaidawa matar ko dai ta shiga bandaki idan amfani za ta yi da shi, ko kuma ta zauna. Haka zalika, daya daga cikin ma’aikatan jirgin ya shaidawa kotun cewa, matar ta tambaye su cewa tana so a bude mata taga, amma lokacin da ta samu amsar da bata yi mat aba sai ta yi amfani da karfinta wajen kokarin bude ...
Sunaye 100 mafiya shahara a kasar Ingila a shekarar 2022 da aka fi sakawa jarirai: Sunan Muhammad ne ya zo na 1

Sunaye 100 mafiya shahara a kasar Ingila a shekarar 2022 da aka fi sakawa jarirai: Sunan Muhammad ne ya zo na 1

Auratayya, labaran duniya na yau
Sunan Muhammad ya zo na 1 a jerin sunaye 100 mafiya shahara da aka fi sakawa jarirai a shekarar 2022 a kasar Ingila.   A bangaren jarirai mata kuwa, Sunan Sophia ne ya zo na daya mafi shahara.   Shafin Babycentre ne ya bayyana haka, kamar yanda jaridar The Mail ta ruwaito.   Cikakken jadawalin sunayen jarirai mata da suka fi shahara: 1. Sophia 2. Lily 3. Olivia 4. Isla 5. Ava 6. Amelia 7. Freya 8. Aria 9. Maya 10. Ivy 11. Emily 12. Isabella 13. Mia 14. Grace 15. Evie 16. Zara 17. Millie 18. Ella 19. Hannah 20. Daisy 21. Rosie 22. Elsie 23. Willow 24. Luna 25. Poppy 26. Zoe 27. Isabelle 28. Sophie 29. Sienna 30. Ada 31. Nur 32. Florence 33. Charlotte 34. Evelyn 35. Emilia 36. Maryam 37. Fatima 38. Harper 39. Phoebe 40....
Zan Yi Wa Yankin Arewa Aiki Kamar Tafawa Balewa, Alkawarin Atiku Ga Mutanan Arewa

Zan Yi Wa Yankin Arewa Aiki Kamar Tafawa Balewa, Alkawarin Atiku Ga Mutanan Arewa

labaran duniya na yau, Siyasa
Daga Abubakar A Adam Babankyauta Dan takarar neman mulkin Nijeriya a karkashin inuwar jam'iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya kai ziyara jihar Gombe don tallata aniyarsa ta gaje kujerar shugaba Buhari a babban zaben 2023. Atiku ya fadi abin da zai yiwa al'ummar jihar Gombe inda ya ce zai zamewa Arewa kamar Abubakar Tafawa Balewa idan dai aka goyi bayan jam'iyyar PDP a zaben 2023. Atiku Abubakar ya yi wa Gombawa alkawarin zai tabbatar da wuta daga madatsar wuta ta Dadin Kowa da ke jihar Gombe idan aka zabe shi a zaben 2023, Alkawarin Atiku Abubakar bai tsaya a iya nan ba domin ya kara tabbatarwa da Gombawa cewa zai gyara duk wata hanyar data hada jihar Gombe da Bauchi Yobe da Gombe Adamawa da Gombe Borno da Gombe domin inganta rayuwar mutanan yankin Arewa maso gabas Atiku ...
An harbe mutum biyar a gidan casu na ƴan Luwadi a Amurka

An harbe mutum biyar a gidan casu na ƴan Luwadi a Amurka

labaran duniya na yau, Tsaro
An harbe mutum biyar a gidan casu na ƴan neman-maza a Amurka Mutum aƙalla biyar ne suka mutu sannan wasu 18 suka jikkata lokacin da wani mutum ya buɗe wuta a wani gidan rawa na 'yan luwaɗi da ke Colorado ta Amurka, in ji 'yan sanda. "Cikin baƙin ciki nake sanar da ku cewa an yi harbe-harbe a wani gidan casun dare a daren nan," in ji kakakin 'yan sanda Pamela Castro. BBC ta rawaito cewa Castro ya ce dakaru sun kai ɗauki "kuma mun ga wani da muke zargi shi ne maharin a cikin kulob ɗin da ake kira Club Q". Club Q ya fitar da sanarwa cewa "mun kaɗu da irin wannan hari na rashin hankali a kan mutanenmu".
Ikon Allah:Kalli Bidiyon yanda wasu Tumaki ke ta dawafi a waje guda a kasar China, sun kwashe kwanaki 12 a haka

Ikon Allah:Kalli Bidiyon yanda wasu Tumaki ke ta dawafi a waje guda a kasar China, sun kwashe kwanaki 12 a haka

labaran duniya na yau
Lamarin ya farune a yankin Mongolia dake kasar inda rahoton ya nunar da cewa kwanaki 12 kanan tumakin na a haka kuma ba'a san dalili ba.   Me dabbobin yace sun fara haka ne ranar 4 ga watan Nuwamba.   Yace da kadan kadan suka fara har suka karu sosai.   Saidai wasu masana sunce wannan lamari cutace wadda kesa dabbobi su haukace. https://www.youtube.com/watch?v=q1jczelQoXE
Abin da ya sa na zama mawaƙin siyasa>>Bashir Ɗandago

Abin da ya sa na zama mawaƙin siyasa>>Bashir Ɗandago

labaran duniya na yau, Siyasa
SHAHARARREN mawaƙin yabon Manzon Allah (s.a.w.) ɗin nan, Malam Bashir Ɗandago ya bayyana dalilin da ya sa shi ma ya bi sahun mawaƙan siyasa, saɓanin yadda aka san shi tsawon shekaru. Ko da yake a wasu lokutan ya na yin wasu waƙoƙin na faɗakarwa ko na jama’a ko sarakuna, kamar waƙar da ya yi wa Sarkin Kano, marigayi Alhaji Ado Bayero, amma dai da sunan siyasa ba a taɓa ji ya yi ba. A ‘yan kwanakin nan sabuwar waƙar da sha’irin ya yi wa jam’iyyar NNPP da ɗan takarar ta na shugaban ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ta cika garin Kano, wanda hakan ya tabbatar da cewa shi ma ya zama mawaƙin siyasa. Mujallar Fim ta tattauna da Bashir Ɗandago a game da shigar sa siyasa da kuma waƙar da ya yi, inda ya ke cewa: “Gaskiya ne na yi waƙar siyasa wadda na yi wa Sanata Rabi’u Musa Kwankwas...
Matata da ‘ya’yana Kirostoci ne, ban Musuluntar da su ba dan haka ku kwantar da hankalinku ba zan musuluntar da Najariya ba>>Tinubu ya gayawa CAN

Matata da ‘ya’yana Kirostoci ne, ban Musuluntar da su ba dan haka ku kwantar da hankalinku ba zan musuluntar da Najariya ba>>Tinubu ya gayawa CAN

labaran duniya na yau, Siyasa
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC,  Bola Ahmad Tinubu ya bayyanawa kungiyar Kiristoci ta CAN cewa bai musuluntar da iyalansa ba, ba zai iya musuluntar da Najariya ba.   Yace matarsa da 'ya'yansa kirostoci ne, kai matarsa ma fastuwa ce, bai tursasa musu musulunci ba dan haka ba zai tursasawa Najariya musulunci ba.   Tinubu yace abin ya masa ciwo da ya ji wasu na cewa wai zai musuluntar da Najariya.