fbpx
Saturday, September 23
Shadow

labaran kaduna ayau

Gwamna Uba Sani na Kaduna ya baiwa Iyamurai 2 mukamai a gwamnatinsa, Ohanaeze Indigbo sun yaba masa

Gwamna Uba Sani na Kaduna ya baiwa Iyamurai 2 mukamai a gwamnatinsa, Ohanaeze Indigbo sun yaba masa

labaran kaduna ayau, Siyasa
Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya baiwa iyamurai 2 mukamai a gwamnatinsa.   Wanda ya baiwa mukaman sune, Mr. Fabian Okoye A matsayin me biwa Gwamna Shawara kan bincike, sai kuma Mrs. Maureen Okogwu-Ikokwu A matsayin babbar me bashi shawara.   Kungiyar Ohanaeze Indigbo reshen jihar Kaduna ta yaba masa.   Shugaban kungiyar, Mazi Chris Emeka Oha yace Gwamna Uba sani yayi abin yabo.
Jami’an tsaron Najeriya sun ‘kashe ƴan fashi huɗu’ a Kaduna

Jami’an tsaron Najeriya sun ‘kashe ƴan fashi huɗu’ a Kaduna

labaran kaduna ayau
Dakarun Sojan Najeriya sun kashe 'yan fashin daji huɗu yayin wani samame da suka kai kan sansanoninsu a Jihar Kaduna. Kwamashinan Tsaro na Kaduna Samuel Aruwan ya ce dakarun da ke cikin rundunar Operation Forest Sanity sun kashe mutanen ne a yankin Ƙaramar Hukumar Chikun. Cikin sanarwar da ya fitar a yau Lahadi, Mista Aruwan ya ce sojoji sun bi sawun 'yan bindigar ne tare da kashe biyu daga cikinsu. Rahotannin sirri da gwamnati ta samu daga yankin sun bayyana cewa ƙarin biyu sun mutu sakamakon raunukan da suka ji, in ji kwamashinan, yayin da rahotannin suka bayyana sunan Dogo Mallam da Bello Mallam cikin 'yan fashin da aka kashe. Ya ƙara da cewa dakarun su ƙwace bindigar AK-47 da babur ɗaya da kuma harsasai.
Masu garkuwa da mutane sun nemi a biyasu Miliyan 10 dan bayar da gawar wanda suka karbi kudin fansarsa kuma suka kasheshi

Masu garkuwa da mutane sun nemi a biyasu Miliyan 10 dan bayar da gawar wanda suka karbi kudin fansarsa kuma suka kasheshi

labaran kaduna ayau, Tsaro
Masu garkuwa da mutane sun nemi a biyasu miliyan 10 kamin su bayar da gawar Obadiah Ibrahim da suka kashe.   Dan uwan mamacin, Kefas Obadiah ne ya bayyanawa manema labarai haka inda yace 'yan Bindigar sun karbi Miliyan 3 amma suka ki sakin dan uwan nasa.   Yace da suka kaiwa 'yan Bindigar miliyan 3 sun gaya musu cewa wadannan kudaden abincine, su je su kawo Miliyan 15.   Yace 'yan Bindigar sun gaya musu sun kashe dan uwansu daga baya saboda kamawa da kuma kashe dan uwansu da 'yansanda suka yi.   Sannan sukace sai an kai musu miliyan 10 kamin su bada gawarsa.
NDLEA ta kama mutum 130 kan miyagun kwayoyi a jihar Kaduna

NDLEA ta kama mutum 130 kan miyagun kwayoyi a jihar Kaduna

labaran kaduna ayau, Tsaro
Hukumar da ke yaki da masu ta'ammali da miyagun kwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta ce ta kama mutum 130 dauke da miyagun kwayoyi a jihar Kaduna a watan Oktoba. Hukumar wadda ta ce bakwai daga cikin mutanen mata ne, kwayoyin sun kai nauyin kilogram 1,728.536. Kwamandan hukumar a jihar ta Kaduna, Mr Umar Adoro, ya gaya wa kamfanin dillancin labarai News Agency of Nigeria yau Laraba cewa, hukumar tasa ta kuma rushe wurare 20 da suka yi kaurin suna wajen hada-hadar miyagun kwayoyi. Haka kuma shugaban ya kara da cewa sun yi nasarar rufe gidaje bakwai da ke da alaka da miyagun kwayoyi. Adoro ya ce hukumar ta kuma gano naira dubu N300 ta takardar naira N1,000 daga wadanda aka kama masu safarar miyagun kwayoyi. Kwamandan ya ce miyagun kwayoyin da aka kwace sun kunshi ganyen wiwi kilogram 1,388....
Wata daya da yin aure, Wata mata ta mayarwa da mijinta Sadakinshi a kashe auren a jihar Kaduna

Wata daya da yin aure, Wata mata ta mayarwa da mijinta Sadakinshi a kashe auren a jihar Kaduna

labaran duniya na yau, labaran kaduna ayau
Kotun shari'ar musulunci dake Magajin Gari jihar Kaduna ta umarni wata mata, Maryam Dahiru data mayarwa da mijinta sadakin 100,000 da kuma akwatin kaya da ya sai mata.   Mai shari'a, Malam Rilwanu Kyaudai ne ya tabbatar da rabuwar auren ta hanyar Khul'i.   Alkalin yace kayan da bata fara sakawa bane kawai zata mayarwa da mijin nata.   Maryam ce dai ta shigar da karan ta hannun lauyanta, Murtala Kyallesu inda tace bata son ci gaba da zama da mijin nata kuma a shirye take ta mayar masa da sadakinsa.   Saidai mijin, Salihu Yakubu, ta hannun lauyansa, M. M. Dahiru ya bayyana cewa, har yanzu yana son matarsa.   Kamfanin dillancin labaran Najariya, NAN ya ruwaito Yakubu na cewa ta dawo masa da duka kayan da ya sai mata na lefe, bayan da ta n...
Canjin kudi ko wani abu makamancinsa ba zai hana garkuwa da mutane ba>>Sheikh Gumi

Canjin kudi ko wani abu makamancinsa ba zai hana garkuwa da mutane ba>>Sheikh Gumi

labaran kaduna ayau, Tsaro
Babban malamin addinin Islama, Sheikh Dr Ahmad Gumi ya bayyana canjin kudin da gwamnati ke shirin yi a matsayin abu me kyau.   Saidai yace a wannan lokaci, ba zai haifarwa kasarnan da me ido ba.   Yace a yanzu haka ma mutane yawanci basu kudin sayen kayan amfani, yace idan kana son sanin hakan, ka tambayi 'yan kasuwa zasu gaya maka.   Yace kuma maganar cewa hakan zai yi maganin 'yan garkuwa da mutane ba gaskiya bane, yace abinda kawai zai magance matsalar shine adalci, da tsaro me kyau, da kuma daidaito wajan rabon dukiyar kasa.
Kotu ta ɗaure matashi ɗan kirifto a Kaduna saboda zamba ta Instagram

Kotu ta ɗaure matashi ɗan kirifto a Kaduna saboda zamba ta Instagram

labaran kaduna ayau
Babbar Kotun Jihar Kaduna ta ɗaure matashi mai harkokin kuɗi ta intanet wato Cryptocurrency tsawon wata uku a gidan yari bayan ta kama shi da laifin zamba. Mai Shari'a Darius Khobo ya yanke wa Emmanuel Simon hukuncin ne a ranar Alhamis bayan hukuamr EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta gurfanar da shi a gaban kotunsa bisa zargin aikata zamba ta intanet. An tuhumi Mista Simon da yin amfani da shafin dandalin zumunta na Instagram ɗauke da sunan Hakc4ord da kuma Mrs Gina daga jihar California ta Amurka. Rahoton shari'ar da EFCC ta wallafa ranar Juma'a ya ce matashin kan tura wa mutane saƙon cewa su zuba jari a harkar kirifto tare da yi musu alƙawarin za su samu riba cikin kwana bakwai.
Yanda iyaye ke baiwa ‘yan Bindiga ‘ya’yansu mata suna lalata dasu ana basu kudi a Kaduna

Yanda iyaye ke baiwa ‘yan Bindiga ‘ya’yansu mata suna lalata dasu ana basu kudi a Kaduna

labaran kaduna ayau
Kwamishiniyar kula da walwala ta jihar Kaduna, Hafsat Baba ta bayar da labarin yanda iyaye ke bada 'ya'yansu mata wajan 'yan Bindiga ana lalata dasu ana basu kudi.   Ta bayyana hakane a Abuja wajan taro kan mata ranar Laraba.   Tace matan dake bayar da 'ya'yansu a matsayin masu aikin gida suna taimakawa yawan yaran da ake samu wanda basa zuwa makaranta.   Ta bayar da misalin alkaluman UNICEF wanda suka nuna yara mata miliyan 10 ne basa zuwa makaranta a Najeriya.   Tace irin yaran da ake dorawa talla zaka gansu akan tituna, abin bakin ciki shine, wani lokacin ma sune ke ciyar da mutanen gidansu.   Ta kara da cewa ta ma samu labarain ana bayar da 'yan mata wajan 'yan Bindiga suna lalata dasu su baiwa iyayen yaran kudi.