
Gwamna Uba Sani na Kaduna ya baiwa Iyamurai 2 mukamai a gwamnatinsa, Ohanaeze Indigbo sun yaba masa
Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya baiwa iyamurai 2 mukamai a gwamnatinsa.
Wanda ya baiwa mukaman sune, Mr. Fabian Okoye A matsayin me biwa Gwamna Shawara kan bincike, sai kuma Mrs. Maureen Okogwu-Ikokwu A matsayin babbar me bashi shawara.
Kungiyar Ohanaeze Indigbo reshen jihar Kaduna ta yaba masa.
Shugaban kungiyar, Mazi Chris Emeka Oha yace Gwamna Uba sani yayi abin yabo.