fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

labaran kano na yau

Kalli Bidiyo: Dan Jam’iyyar APC Anas Abba Dala ya nemi yan jam’yyar da su zabi NNPP maimakonta.

Kalli Bidiyo: Dan Jam’iyyar APC Anas Abba Dala ya nemi yan jam’yyar da su zabi NNPP maimakonta.

labaran kano na yau
Dan Jam'iyyar APC Anas Abba Dala ya nemi yan jam'yyar da su zabi NNPP maimakonta. A cewarsa jam'iyyar bata kyautawa mutanen Kano ba, kuma zabar Abba Kabir na NNPP shi zai farfado da kimar jihar. Ya kara da cewa, ya kewaya yankunan Kano da dama kuma ya fahimci jama'a sun dawo daga rakiyar APC. Ga dai Anas Abba Dalan: Dan Jam'iyyar APC Anas Abba Dala ya nemi yan jam'yyar da su zabi NNPP maimakonta. https://youtu.be/W8vN4WgKHvY
Ana fargaba a Kano saboda rikicin dake faruwa tsakanin jam’iyyun siyasa yayin da zaben gwamna ke karatowa

Ana fargaba a Kano saboda rikicin dake faruwa tsakanin jam’iyyun siyasa yayin da zaben gwamna ke karatowa

labaran kano na yau
Ana zaman dardar a Kano yayin da zaba gwamna ke karatowa saboda rikicin da ake samu tsakanin jam'iyyun siyasa a jihar.   Tuni dai hukumar 'yansanda ta jihar ta sanar da cewa ta samu bayanan sirri masu nuni da cewa wasu na son kawo bata gari jihar dan hargitsa lamura yayin zaben gwamnoni.   Duka dai jam'iyyun siyasa a jihar na zargin juna wajan yunkurin tayar da fitina.   Kuma idan ba a dauki mataki ba, abinda ya faru a zaben gwamna na shekarar 2019 ka iya maimaita kansa kamar yanda Daily Trust ta ruwaito.   Tuni dai kwamishinan 'yansandan jihar, Mamman Dauda ya gargadi masu son tada fitina a yayin zaben da su kuka da kansu dan kuwa hukumar tasu ba zata yi kasa a gwiwa ba wajan tabbatar da zaman lafiya a yayin zaben.
Mutum 1 ya rasu, 4 sun jikkata, sakamakon cizon Kare a Kano

Mutum 1 ya rasu, 4 sun jikkata, sakamakon cizon Kare a Kano

labaran kano na yau
Wani matashi ya rasa ransa, huɗu kuma sun jikkata sakamakon cizon da wani mahaukacin kare ya yi musu a unguwar Ƙofar Ɗan Agundi da ke Kano. Wanda ya rasu din sunansa, Faruq Usman, kamar yanda kafar Freedom Radio ta ruwaito.   Dan uwan mamacin ya shaidawa majiyar tamu cewa wata daya kenan da karen ya ciji Faruq amma bai fada ba sai daga baya.   Dalili kenan da ciwon ya shiga jikinsa sosai.   Dayan da karen ya ciza shima yana can Asibiti, rai hannun Allah, sai kuma sauran ukun suna nan suna harkokinsu amma an musu allurar rigakafi.   Tuni dai matasa suka kashe wannan karya.   Wani masani da aka zanta dashi akan lamarin yace idan kare yayi cizo irin wannan, kamata yayi a kai karen da wanda ya ciza Asibiti cikin gaggawa
Kalli Bidiyo yanda dan majalisar jihar Kano, Alhassan Ado Doguwa ke gayawa mabiyansa cewa ranar zabe ko dai mutum ya zabi APC ko ya ci Ubansa

Kalli Bidiyo yanda dan majalisar jihar Kano, Alhassan Ado Doguwa ke gayawa mabiyansa cewa ranar zabe ko dai mutum ya zabi APC ko ya ci Ubansa

labaran kano na yau
Bulaliyar majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa ya bayyanawa magoya bayansa a jihar Kano cewa, ranar Zabe a fito, ko dai mutum ya zabi APC ko ya ci ubansa ne.   Ya bayyana haka a wani bidiyo da aka gani wanda kafar Leadership Hausa ta wallafa. https://twitter.com/LeadershipNGA/status/1600060049467940865?t=9E9Hfhwz0R9j_IoOGS-XpQ&s=19  
Hatsari Ya Faru A Hanyar Titin Garin Malam Tsakanin Mai karamin mota Da me Tanki Wannan Abun da Kuke Gani Acikin Buhu Mutum Biyu Aka Hade Acikin buhu, Duk Sun Rasu Allah Ubangiji Yayi Musu Rahama

Hatsari Ya Faru A Hanyar Titin Garin Malam Tsakanin Mai karamin mota Da me Tanki Wannan Abun da Kuke Gani Acikin Buhu Mutum Biyu Aka Hade Acikin buhu, Duk Sun Rasu Allah Ubangiji Yayi Musu Rahama

labaran kano na yau
Innallillahi Wa, innallillahi Ra'jun Hatsari Ya Faru A Hanyar Titin Garin Malam Tsakanin Mai karamin mota Da me Tanki Wannan Abun da Kuke Gani Acikin Buhu Mutum Biyu Aka Hade Acikin buhu, Duk Sun Rasu Allah Ubangiji Yayi Musu Rahama. Daga: Comrd Usama Lere kura Daga Shafin Sahihiya. Kalli karin hotuna da bidiyo a kasa: https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=pfbid09zeXJpYMbrzwxSWh9e4P3LeGpULpJmxGoTbYkqQAvmcjdD9QaUH1u1ARYykudrY1l&id=100075543998029   https://fb.watch/hby8PLyONt/   https://fb.watch/hbyaQb4SLG/
‘Kalamaina na ‘ko da tsiya-tsiya’ ba na tunzura rikici ba ne’

‘Kalamaina na ‘ko da tsiya-tsiya’ ba na tunzura rikici ba ne’

labaran kano na yau, Siyasa
Shugaban jam'iyyar APC reshan jihar Kano, Abdullahi Abbas ya musanta zarge-zargen da ake masa na amfani da kalaman tunzura gangamin yaƙin neman zaɓe da tarukan siyasa. Kalmar "ko da tsiya ko da tsiya-tsiya, sai mun ci zaɓe", ba baƙon abu ne domin an sha jiyo Abdullahi Abbas na ambato wadannan kalamai a tarukan siyasa tun daga zaben 2019. Ƴan adawa a jihar na cewa irin wadannan kalamai na Abdullahi Abbas, wata alama ce da ke nuna cewa mai yiwuwa akwai wani mummunan nufi da APC ta yi game da babban zaɓe da ke tafe a jihar. Sai dai a tattaunawarsa da BBC, shugaban APCn a Kano ya ce an yi wa maganganunsa mummunar fahimta ce kawai. A makon da ya gabata ne BBC ta kawo rahoto kan zargin da ake yi wa shugaban jam'iyyar APC na yin kalaman tunzura rikici. "Galats...
Cece-kuce ya ɓarke a jam’iyyar PDP ta Kano bayan wani taron masu ruwa da tsakin jagororinta a gidan tsohon Gwamna Malam Ibrahim Shekarau

Cece-kuce ya ɓarke a jam’iyyar PDP ta Kano bayan wani taron masu ruwa da tsakin jagororinta a gidan tsohon Gwamna Malam Ibrahim Shekarau

labaran kano na yau
Cece-kuce ya ɓarke a jam'iyyar PDP ta Kano bayan wani taron masu ruwa da tsakin jagororinta a gidan tsohon Gwamna Malam Ibrahim Shekarau. Rahotonni sun ce, mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan jam'iyyar Yusuf Bello Ɗanbatta ya je gidan amma ba a amince ya shiga taron ba, kasancewar baya cikin waɗanda aka gayyata. Da alama kuma wannan ne ya hassala magoya bayansa, inda suka shiga musayar kalamai da mabiyan Malam Shekarau musamman a kafafen sada zumunta. Freedom Radio.