fbpx
Saturday, September 23
Shadow

labaran katsina na yau

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Da Sace Matan Aure 10 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Da Sace Matan Aure 10 A Katsina

labaran katsina na yau, Tsaro
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Da Sace Matan Aure 10 A Katsina A daren Alhamis ɗin da ta gabata, yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a kauyen Katsalle da ke gundumar Rafin Iwa ta ƙaramar hukumar Sabuwa a jihar Katsina, inda suka kashe Malam Khalid Alhaji Saleh, ɗan shekara arba'in da biyar da haihuwa da kuma sace matan aure Goma. Majiyar RARIYA ta naƙalto cewa yan bindigar sun je garin Katsalle da misalin karfe ɗayan daren Alhamis, da shigar su suka fara harbe-harbe ba kyaf-kyaftawa, inda suka kashe mutum daya da kuma sace matan aure guda goma. Har zuwa haɗa wannan rahotan, yan bindigar ba su tuntuɓi iyalan wadanda suka sace ba. Allah ya kuɓutar da su cikin Aminci!
Gwamna Masari Ya Aurar Da Ya’yansa Maza Guda Biyu

Gwamna Masari Ya Aurar Da Ya’yansa Maza Guda Biyu

labaran katsina na yau
Gwamna Masari Ya Aurar Da Ya'yansa Maza Guda Biyu Gwamnan Jihar Katsina Alhaji Aminu Bello Masari Ya Aurar Da Ya'yansa Maza Biyu, Muhammad Khaleed Aminu Bello Masari Da Amaryarsa, Husaina Rabe Sani Store Akan Sadaki Naira Dubu Ɗari Da Hamsin, An Ɗaura Auren A Gidan Marigayi Alhaji Sani Store Dake Unguwar Yar'adua Cikin Garin Katsina Da Kuma Abubakar Aminu Bello Masari Da Amaryarsa Maryam Sani Lawal Akan Sadaki Naira Dubu Ɗari Ukku, An Ɗaura Auren Ne A Masallacin Adoro Cikin Garin Katsina Duk A Yau Asabar. Allah Ya Ba Da Zaman Lafiya Da Zuri'a Dayyaba! Daga Jamilu Dabawa, Katsina Rariya.
Kanin Surajo Mai Asharalle Ya Rasu A Katsina

Kanin Surajo Mai Asharalle Ya Rasu A Katsina

labaran katsina na yau
INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Kanin Surajo Mai Asharalle Ya Rasu A Katsina Allah Ya Yi Wa Alhaji Bashir Na'aja, Wanda Kane Ne Ga Shahararren Mawaƙin Asharalle, Alhaji Surajo Mai Asharalle Rasuwa. Za'a Yi Jana'izarsa Da Misalin Karfe 11:00 Na Safiyar Yau Asabar A Gidansa Dake Kusa Da Gidan Alhaji Surajo Mai Asharalle, Kofar Kaura Katsina. Allah Ya Jikansa Da Rahama! Daga Jamilu Dabawa, Katsina Daga Rariya.
Ɓarayin daji a Katsina sun ɗauki aniyar shirya gagarumin mauludi

Ɓarayin daji a Katsina sun ɗauki aniyar shirya gagarumin mauludi

labaran katsina na yau, Tsaro
A shekaran jiya ne ɓarayin dajin dake yankunan Ɗan-musa jihar Katsina suka ɗauki aniyar yin mauludi. Rahoton na cigaba da cewa, Amma sai dai wani shugaban Daba wanda ake kira da Oga hizga ya kafe yace bai yarda suyi wannan mauludi ba harsai sun saya masa sabon mashin. To amma kuma su ɓarayin da suke son shirya mauludin sun kafe cewa, baza su sayawa shi ɗan Daban mashin ɗin ba, daga nan ne dai tarzoma ta tashi tsakanin shi da yaran shi da kuma masu son shirya mauludin wato ɓarayin.” ALFIJIR HAUSA ta bibiyi lamarin inda ta ƙara samun wani labari na ɓallewar rikici tsakanin Ƴan fashin dajin da shi tawagar hizga, Ƴan fashin dajin sun samu nasarar kashe Oga hizga ɗin da kuma kashe wayansu yaran shi guda huɗu, Amma kuma shedun gani da ido sun shaidawa ALFIJIR HAUSA cewa daga cikin yaran...
Mataimakin Shugaban Kungiyar Izala Na Jihar Katsina Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Kungiyar Izala Na Jihar Katsina Ya Rasu

labaran katsina na yau, Uncategorized
INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Mataimakin Shugaban Kungiyar Izala Na Jihar Katsina Ya Rasu Allah Ya Yi Wa Malamin Addinin Musulunci Kuma Mataimakin Shugaban Kungiyar Jama'atul Izalatul Bid'a Wa'ikamatu Sunnah Na Jihar Katsina II, Malam Muhammadu Alti Rasuwa Yau Litinin. Za'a Yi Jana'izarsa Da Misalin Karfe 4:00 Na Yammacin Yau Litinin A Masallacin Juma'a Na Modibbo (Kandahar) Dake Kofar Kaura Cikin Garin Katsina. Allah Ya Jikansa Da Rahama! Daga Jamilu Dabawa, Katsina
An tura jami’an tsaro domin ceto manoman da aka sace a Katsina

An tura jami’an tsaro domin ceto manoman da aka sace a Katsina

labaran katsina na yau, Tsaro
Hukumomi a Najeriya sun ce an tura jami'an tsaron ƙasar domin ceto mutane sama da 20 waɗanda ƴan bindiga suka sace a wata gona da ke jihar Katsina. Cikin mutanen da aka sacen har da mata da dama. Mazauna yankin da abin ya faru sun ce maharan sun zo ne da yawa a kan babura inda suka dirar wa masu girbin amfanin gona a kusa da ƙauyen Mairuwa da ke jihar. Mai magana da yawun rundunar ƴansandan Najeriya a jihar ta Katsina ya shaida wa BBC cewa mutane 21 aka sace a lokacin harin wanda aka kai a ranar Lahadi. Sai dai wasu bayanan na cewa yawan mutanen da aka sacen ya zarce haka.