fbpx
Saturday, September 23
Shadow

labarin zamfara ayau

‘Yadda ‘yan bindiga suka sace mana zawarawa da ‘yan mata 23 a Zamfara’

‘Yadda ‘yan bindiga suka sace mana zawarawa da ‘yan mata 23 a Zamfara’

labarin zamfara ayau, Tsaro
A tsakiyar makon nan ne, wasu 'yan bindiga suka sace zawarawa da 'yan mata da ƙananan yara, wadanda yawansu ya kai 23, a yankin Ƙaramar Hukumar Maradun ta jihar Zamfara. A ranar Laraba ne lamarin ya faru, amma nisa da rashin samun yadda bayanai za su fita ya sa ba a ji labarin sace matan ba sai a jiya Alhamis. Mazauna yankin Muradun na kukan cewa ayyukan 'yan fashin daji da ake ta yaɗa cewa sun ragu "ba haka abin yake ba" kawai dai ji ne ba a yi. Wani magidanci da BBC ta zanta da shi da ya nemi a ɓoye sunansa saboda tsaro, ya ce "matan sun fita bayan gari ne yin itace suka ci karo da 'yan bindigar. "Duk safiya suna tafiya daji yin itace, a wannan karon tawaga ce ta zawarawa da 'yan mata da matan da mazajensu suka mutu da kuma ƙananan yara abin ya rutsa da su. ...
Da Duminsa: Bam din da ‘yan Bindiga suka dasa ya kashe hatsabibin dan Bindiga a jihar Zamfara, Watau Dogo Gudali

Da Duminsa: Bam din da ‘yan Bindiga suka dasa ya kashe hatsabibin dan Bindiga a jihar Zamfara, Watau Dogo Gudali

labarin zamfara ayau, Tsaro
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa, wani bam da 'yan Bindiga suka dasa ya tashi da hatsabibin dan Bindiga, Dogo Gudali inda ya mutu.   Rahoton yace, yaran dan bindigar ne suka dasa bam din daya kasheshi.   Wani jami'in soja ya bayyana cewa 'yan Bindigar sun dasa bam dinne dan kashe sojoji.   Rundunar soji dai ta Hadarin Daji na kan bibiya da kakkabe burbushin 'yan Bindigar.
Kalli Gidan gwamnatin jihar Zamfara da aka kwashe komai a cikinsa

Kalli Gidan gwamnatin jihar Zamfara da aka kwashe komai a cikinsa

labarin zamfara ayau, Siyasa
Bidiyo ya bayyana a shafukan sada zumunta wanda aka ce na gwamnatin jihar Zamfara ne dake Abuja.   An ga cewa an kwashe komai na gidan.   An dai zargi tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle da mukarrabansa da yin wannan aika-aika.   Dama dai Gwamna Lawal Dare ya zargi cewa tsohon gwamnan ya tafi da motoci na Bikiyoyin Naira mallakin gwamnatin jihar inda yace ya bashi lokaci ya dawo dadu.    
An gano gawarwakin mutane 213 a Zamfara bayan artabu tsakanin Sojoji da ‘yan Bindiga

An gano gawarwakin mutane 213 a Zamfara bayan artabu tsakanin Sojoji da ‘yan Bindiga

labarin zamfara ayau, Tsaro
Akalla gawarwakin mutane 213 ne aka samu bayan musayar wuta data faru tsakanin 'yan Bindiga da sojojin Najariya a Jihar Zamfara.   Hakanan sojoji 10 sun rasa rayukansu a wannan kazamin artabun kamar yanda kafar PRNigeria ta ruwaito.   Lamarin ya farune a yankin Malele Dansadau inda kuma rahoton yace an kashe 'yan Bindigar da yawa.   Sojojin sama dana kasa ne suka yi artabu da 'yan Bindigar wanda lamarin ya kare da nasara akan 'yan Bindigar.   Ana dai yawan samun matsalar fadan fulani da manoma a yankunan Malele, Maigoge, Yan Sawayu, Ruwan Tofa, Mai Awaki, da Zama Lafiya na jihar wanda ya mayar da yankin me matukar hadari.
Dakarun Najeriya sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a Zamfara

Dakarun Najeriya sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a Zamfara

labarin zamfara ayau
Dakarun shirin sharan daji da ake kira FOREST SANITY sun ce sun yi artabu da ƴan bindiga a yankin Danmarke na ƙaramar hukumar Gummi ta jihar Zamfara lokacin da suke sintiri a yankin. Sanarwar da sojojin Najeriyar suka fitar a ranar Alhamis ta ce a lokacin artabun ƴan bindigan sun tsere suka bar maɓuyarsu da makamai, yayin da da dama daga cikin su suka samu raunin harbin bindiga. Dakarun sun samu nasarar kuɓutar da mutum uku, da ƙwato bindigogi ƙirar AK47 guda biyar, da kuma babura 30. BBChausa.
Ana wahalar man fetur a Zamfara, Lamarin yasa tsadar Rayuwa

Ana wahalar man fetur a Zamfara, Lamarin yasa tsadar Rayuwa

labarin zamfara ayau, Siyasa
Matsanancin karancin Man fetur ya shiga jihar Zamfara inda hakan yasa rayuwa ta yi tsada.   Wasu 'yan kasuwa sun bayyanawa majiyarmu cewa, dalilin haka mutane basa zuwa sayen kaya sosai kamar a baya.   Hakanan wasu mutane a jihar dole sun koma tafiyar kafa saboda abin hawa yayi tsada.   Wani da aka zanta dashi yace shi da iyalansa ba zasu yi zabe a shekarar 2023 ba saboda basu ga ribar dimokradiyya ba.   Yace ya kammala aiki na shekaru 35 a jihar inda ake biyansa albashin Naira N7,500 yace ta yaya kasarnan zata gyaru yayin da masu kudi ke kara kudancewa, talaka kuma na kara shiga halin ha'ula'i?
Da Duminsa:Kotu ta hana jam’iyyar PDP shiga zaben Gwamna a jihar Zamfara

Da Duminsa:Kotu ta hana jam’iyyar PDP shiga zaben Gwamna a jihar Zamfara

labarin zamfara ayau, Siyasa
Kotun gwamnatin tarayya dake Gusau ta soke zaben dan takarar gwamna na jihar Zamfara, Dauda Lawan-Dare, inda kuma tace ba za' mayeshi da wani dan takarar ba.   Mai shari'a, Aminu Bappa ne ya yanke wannan hukunci ranar Talata. Inda yace jam'iyyar PDP ba zata fitar da wani dan takarar ba a zaben 2023.   Wannan ne karo na biyu da kotu ke soke 'yan takarar gwamna na jihar ta Zamfara.   Koda a watan Satumba da ya gabata, sai da kotun ta soke zaben fidda gwani na jam'iyyar ta PDP a jihar.
‘Yan Bindiga sun sace mutane a Zaria, Zamfara, da Naija

‘Yan Bindiga sun sace mutane a Zaria, Zamfara, da Naija

labaran duniya na yau, labarin zamfara ayau, Tsaro
A Zaria, 'yan Bindigar sun je Kofar Gayan ne inda suka sace mutane 6.   Yankin dama ya sha fama da masu garkuwa da mutane. Daily trust ta ruwaito cewa da Misalin kargi 11: 30 ne dai 'yan Bindigar suka kai harin.   Sun rika harbi a iska har suka tafi da wadanda suka sace din.   A jihar Zamfara kuwa, mutane 4 ne aka sace a Dama dake karamar hukumar Gusau.   Biyu daga cikin wanda aka sace, dalibai ne a jami'ar gwamnatin tarayya dake Gusau din.   Hakanan 'yan Bindigar sun sace wani Shehu Usman Wanda ma'aikacin lafiyane a babban Asibitin Kagara.