fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

labarin zamfara ayau

An gano gawarwakin mutane 213 a Zamfara bayan artabu tsakanin Sojoji da ‘yan Bindiga

An gano gawarwakin mutane 213 a Zamfara bayan artabu tsakanin Sojoji da ‘yan Bindiga

labarin zamfara ayau, Tsaro
Akalla gawarwakin mutane 213 ne aka samu bayan musayar wuta data faru tsakanin 'yan Bindiga da sojojin Najariya a Jihar Zamfara.   Hakanan sojoji 10 sun rasa rayukansu a wannan kazamin artabun kamar yanda kafar PRNigeria ta ruwaito.   Lamarin ya farune a yankin Malele Dansadau inda kuma rahoton yace an kashe 'yan Bindigar da yawa.   Sojojin sama dana kasa ne suka yi artabu da 'yan Bindigar wanda lamarin ya kare da nasara akan 'yan Bindigar.   Ana dai yawan samun matsalar fadan fulani da manoma a yankunan Malele, Maigoge, Yan Sawayu, Ruwan Tofa, Mai Awaki, da Zama Lafiya na jihar wanda ya mayar da yankin me matukar hadari.
Dakarun Najeriya sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a Zamfara

Dakarun Najeriya sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a Zamfara

labarin zamfara ayau
Dakarun shirin sharan daji da ake kira FOREST SANITY sun ce sun yi artabu da ƴan bindiga a yankin Danmarke na ƙaramar hukumar Gummi ta jihar Zamfara lokacin da suke sintiri a yankin. Sanarwar da sojojin Najeriyar suka fitar a ranar Alhamis ta ce a lokacin artabun ƴan bindigan sun tsere suka bar maɓuyarsu da makamai, yayin da da dama daga cikin su suka samu raunin harbin bindiga. Dakarun sun samu nasarar kuɓutar da mutum uku, da ƙwato bindigogi ƙirar AK47 guda biyar, da kuma babura 30. BBChausa.
Ana wahalar man fetur a Zamfara, Lamarin yasa tsadar Rayuwa

Ana wahalar man fetur a Zamfara, Lamarin yasa tsadar Rayuwa

labarin zamfara ayau, Siyasa
Matsanancin karancin Man fetur ya shiga jihar Zamfara inda hakan yasa rayuwa ta yi tsada.   Wasu 'yan kasuwa sun bayyanawa majiyarmu cewa, dalilin haka mutane basa zuwa sayen kaya sosai kamar a baya.   Hakanan wasu mutane a jihar dole sun koma tafiyar kafa saboda abin hawa yayi tsada.   Wani da aka zanta dashi yace shi da iyalansa ba zasu yi zabe a shekarar 2023 ba saboda basu ga ribar dimokradiyya ba.   Yace ya kammala aiki na shekaru 35 a jihar inda ake biyansa albashin Naira N7,500 yace ta yaya kasarnan zata gyaru yayin da masu kudi ke kara kudancewa, talaka kuma na kara shiga halin ha'ula'i?
Da Duminsa:Kotu ta hana jam’iyyar PDP shiga zaben Gwamna a jihar Zamfara

Da Duminsa:Kotu ta hana jam’iyyar PDP shiga zaben Gwamna a jihar Zamfara

labarin zamfara ayau, Siyasa
Kotun gwamnatin tarayya dake Gusau ta soke zaben dan takarar gwamna na jihar Zamfara, Dauda Lawan-Dare, inda kuma tace ba za' mayeshi da wani dan takarar ba.   Mai shari'a, Aminu Bappa ne ya yanke wannan hukunci ranar Talata. Inda yace jam'iyyar PDP ba zata fitar da wani dan takarar ba a zaben 2023.   Wannan ne karo na biyu da kotu ke soke 'yan takarar gwamna na jihar ta Zamfara.   Koda a watan Satumba da ya gabata, sai da kotun ta soke zaben fidda gwani na jam'iyyar ta PDP a jihar.
‘Yan Bindiga sun sace mutane a Zaria, Zamfara, da Naija

‘Yan Bindiga sun sace mutane a Zaria, Zamfara, da Naija

labaran duniya na yau, labarin zamfara ayau, Tsaro
A Zaria, 'yan Bindigar sun je Kofar Gayan ne inda suka sace mutane 6.   Yankin dama ya sha fama da masu garkuwa da mutane. Daily trust ta ruwaito cewa da Misalin kargi 11: 30 ne dai 'yan Bindigar suka kai harin.   Sun rika harbi a iska har suka tafi da wadanda suka sace din.   A jihar Zamfara kuwa, mutane 4 ne aka sace a Dama dake karamar hukumar Gusau.   Biyu daga cikin wanda aka sace, dalibai ne a jami'ar gwamnatin tarayya dake Gusau din.   Hakanan 'yan Bindigar sun sace wani Shehu Usman Wanda ma'aikacin lafiyane a babban Asibitin Kagara.  
‘Yan sanda sun daƙile hare-haren ‘yan bindiga a Zamfara

‘Yan sanda sun daƙile hare-haren ‘yan bindiga a Zamfara

labarin zamfara ayau
Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce ta samu nasarar daƙile hare-haren 'yan bindiga a faɗin ƙananan hukumomin jihar guda hudu, tare da kuɓutar da wasu mutum huɗu da aka yi garkuwa da su. A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar SP Mohammed Shehu, ya fitar ya ce 'yan bindigar sun yi ƙoƙarin kai hare-hare a wasu ƙauyuka da ke ƙananan hukumomin Maru, da Bungudu, da Tsafe da kuma ƙaramar hukumar Bukkuyum. Ya ce jami'ansu sun samu nasarar daƙile hare-haren ta hanyar bayanan sirri da suka samu. SP Mohammed Shehu, ya ƙara da cewa daga ranar Juma'a zuwa Lahadi sun samu bayanan sirri da ke nuna cewa 'yan bindigar na shirin ƙaddamar da hare-hare tare da mutane a ƙauyukan da ke wanɗannan ƙananan hukumomi.
Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukucin Share Masallacin Juma’a A Garin Gusau Saboda Ya Mari Malamin Makarantar Islamiyya

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukucin Share Masallacin Juma’a A Garin Gusau Saboda Ya Mari Malamin Makarantar Islamiyya

labarin zamfara ayau, Uncategorized
Daga Hajiya Mariya Azare Wata babbar kotun addinin islama ta yankewa wani magidanci hukuncin share masallacin Juma'a a garin Gusau dake jihar Zamfara saboda ya mari malamin lslamiya. Kotun ta yanke wannan hukuncin ne biyo bayan tuhumar mutumin da marin malamin makarantan islamiyan da yake koyar da 'yarsa. Alkalin kotun ya ce "tunda Allah ya sa kai ma musulmi ne gashi kuma gobe Juma'a to hukuncin ka shine, ka je ka share ciki da wajen wani babban masallacin Juma'a. Daga Rariya.
Dan PDP a Zamfara, Alhaji Mas’ud Danguruf ya koma APC

Dan PDP a Zamfara, Alhaji Mas’ud Danguruf ya koma APC

labarin zamfara ayau, Siyasa
Ɗan siyasa, shahararren ɗan kasuwa Alhaji Mas'ud Ɗanguruf yayi zama na musamman da ɗan takarar shugaban kasar Najeriya ƙarƙashin jam'iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Alhaji Mas'ud Ɗanguruf wanda jigo ne a jam'iyyar PDP kuma na hannun daman Atiku Abubakar da ya bada gudunmawa wajen yaƙin neman zaɓen shi a zaɓen shekarar 2019. Tun bayan ɓullar hotunan ɗanguruf da Gwamnan Zamfara Governor Bello Matawalle a farkon sati anyi ta ce-ce-kuce akan giɓin da Ɗanguruf zai bari a jam'iyyar PDP idan har ta tabbata yabar jam'iyyar kasancewar shi jigo acikin ta.
Abin Alfahari:’Yar Najariya, Khadija Haliru ta fito takarar Kansila a kasar Canada kuma ta lashe zaben

Abin Alfahari:’Yar Najariya, Khadija Haliru ta fito takarar Kansila a kasar Canada kuma ta lashe zaben

labarin zamfara ayau, Siyasa
Wannan wata 'yan Najariya ce data fito takarar Kansila a yankin Ingersoll dake Ontario na kasar Canada.   Kuma ta yi nasara.   Mina taya Khadija Mamudu-Haliru Murna. Nigerian in Diaspora. Nana Khadijah Mamudu-Haliru has done us proud.. She contested for councullorship in Ingersoll of Ontario council in far away Canada and has won..Congrats #ProudlyNigerian https://t.co/AiDAkNEf4R