
‘Yadda ‘yan bindiga suka sace mana zawarawa da ‘yan mata 23 a Zamfara’
A tsakiyar makon nan ne, wasu 'yan bindiga suka sace zawarawa da 'yan mata da ƙananan yara, wadanda yawansu ya kai 23, a yankin Ƙaramar Hukumar Maradun ta jihar Zamfara.
A ranar Laraba ne lamarin ya faru, amma nisa da rashin samun yadda bayanai za su fita ya sa ba a ji labarin sace matan ba sai a jiya Alhamis.
Mazauna yankin Muradun na kukan cewa ayyukan 'yan fashin daji da ake ta yaɗa cewa sun ragu "ba haka abin yake ba" kawai dai ji ne ba a yi.
Wani magidanci da BBC ta zanta da shi da ya nemi a ɓoye sunansa saboda tsaro, ya ce "matan sun fita bayan gari ne yin itace suka ci karo da 'yan bindigar.
"Duk safiya suna tafiya daji yin itace, a wannan karon tawaga ce ta zawarawa da 'yan mata da matan da mazajensu suka mutu da kuma ƙananan yara abin ya rutsa da su.
...