fbpx
Thursday, October 5
Shadow

Laifuka

An gurfanar dashi saboda yiwa karamin yaro luwadi ta karfin tsiya a jihar Adamawa

An gurfanar dashi saboda yiwa karamin yaro luwadi ta karfin tsiya a jihar Adamawa

Laifuka
An gurfanar da Sani Salihu dan shekaru 45 a gaban kotu a jihar Adamawa saboda yin luwadi da karamin yaro me shekaru 14.   Wanda ake zargin dai ya fito ne daga kauyen Juppa Jam na karamar hukumar Yola.   Saidai ya ki amsa laifinsa, alkalin kotun ya dage sauraren karar sai 20 ga watan Yuli inda yace a kai wanda ake zargi gidan yari.   Hakanan an yanke masa hukuncin daurin shekaru 2 a gidan yari ko biyan tarar Naira 100 akan laifin kokarin tserewa yayin da aka kamashi.    
Aikin Dana Sani:Magidanci ya kashe dansa da duka saboda fitsarin kwace a jihar Borno

Aikin Dana Sani:Magidanci ya kashe dansa da duka saboda fitsarin kwace a jihar Borno

Laifuka
Wani magidanci ya kashe dansa da Duka saboda fitsarin kwance a jihar Born.   Lamarin ya farune a makon da ya gabata, kamar yanda jaridar Daily Trust ta ruwaito.   Wanda yayi wannan aika-aika sunansa, Muhammed Jubrin.   Mahaifin wanda yayi kisan watau kakan wanda aka kashe ne ya sanar da lamarin inda yace dan nasa ya buga kan jikansa a bango.   An garzaya da yaron me shekaru 6 Asibiti inda acan aka tabbatar da cewa ya mutu.   Tuni dai jami'an tsaro suka kamashi.
An kama wani Ɓarawon wayar iPhone 13 a Gidan biki

An kama wani Ɓarawon wayar iPhone 13 a Gidan biki

Laifuka
  An kama wani Ɓarawon wayar iPhone 13 a Gidan biki A jiya ne dai wani Video na wata mata data rinka kururuwar an sace Mata waya a wajan Fatty na biki, ya zagaya kafafen sada zumunta. Sai da a wani sabon Videon kuma da wasu matasa suka saki a TikTok sunce sun kama ɓarawon ne lokacin da yazo siyar da wayar a kasuwa, inda sukai alkawarin miƙa shi ga yan sanda. Meye Ra'ayin ku?
Ana zargin Fasto da yiwa ‘yar shekaru 19 fyade da kasheta bayan da ta je neman ya kara mata tsawon rai

Ana zargin Fasto da yiwa ‘yar shekaru 19 fyade da kasheta bayan da ta je neman ya kara mata tsawon rai

Laifuka
Ana zargin wani fasto me suna Omotayo Valentine Akingbesote Da kashe wata yarinya me suna Loveth da ta je ya mata Addu'ar tsawon rai.   Lamarin ya farune a Igunshin dake jihar Ondo inda aka kama mutumin me shekaru 65.   Ya dai yiwa yarinyar wayau ne ya bata kwaya ta sha wadda yace mata wai itace zata sa ta samu tsawon rai.   Kakakin 'yansandan jihar, Funmilayo Odunlami-Omisanya ta tabbatar da faruwar lamarin inda tace suna kan binciken faston.
Kotu ta yanke wa mutum 4 hukuncin kisa sakamakon kama su da laifin kisa

Kotu ta yanke wa mutum 4 hukuncin kisa sakamakon kama su da laifin kisa

Laifuka
Kotu ta yanke wa mutum 4 hukuncin kisa sakamakon kama su da laifin kisa Wata babbar kotun jihar Jigawa dake zama a garin Ringim ta yanke wa wasu mutane huɗu hukuncin kisa ta hanyar rataya, sakamakon kama su da laifin kisan kai. Waɗanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da, Salahu Ya’u, Aminu Salmanu, Salmanu Shafi’u da kuma Yusuf Sake dukkanin su mazauna ƙauyen Kalawa dake yankin ƙaramar hukumar ta Ringim. Gaskiya Ta Fi Kwabo ta ruwaito cewa tun da fari an gurfanar da mutanen ne kan zargin kisan kai da yin taro ba bisa ka’ida ba, da haɗa baƙi wajen aikata ta’addanci. Da ya ke yanke hukuncin Alkalin kotun mai shari’a Ahmad Muhammad Abubakar, ya ce, laifin da suka aikata ya saɓa da sashe na 100 da 342, da kuma 221 na dokokin penal code na jihar....
Magidanci ya gogawa diyar bazawarar da yake nema me shekaru 8 cutar Kanjamau bayan da ya mata fyade

Magidanci ya gogawa diyar bazawarar da yake nema me shekaru 8 cutar Kanjamau bayan da ya mata fyade

Laifuka
Bazawarar da diyarta me shekaru 8 sun kamu da cutar Kanjamau bayan da bazawarinta, wanda yana da aure me suna, Jude Chinedu yawa diyarta Fyade.   Lamarin ya farune a Alegbor dake karamar hukumar Uvwie a jihar Delta.   Mutumin dai na zaune tare da matar ne a gidan da take, saidai da labarin cewa yawa karamar yarinyar fyade ya bayyana, sai ya tsere.   'Yansanda dai na bibiyar sahunsa.
HARIN JIRGIN ƘASAN ABUJA: Kotu ta ƙi bayar da belin Tukur Mamu

HARIN JIRGIN ƘASAN ABUJA: Kotu ta ƙi bayar da belin Tukur Mamu

Laifuka
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi fatali da neman belin da Tukur Mamu ya shigar ta hannun lauyan sa. An kama Tukur Mamu watanni bakwai da su ka gabata, dangane da hannun da ake zargin ya na da shi wajen kusanci ko alaƙa da ‘yan ta’addar da su ka kai hari kan jirgin ƙasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna. Mai Shari’a Inyang Ekwo ya ce iƙirarin da aka yi cewa Mamu ba shi da lafiya, ba gamsassun dalilan da kotu za ta iya amincewa ba ne har ta bayar da belin wanda ake tuhuma da laifin da ya danganci ta’addanci. An kama Mamu bisa zargin kusanci da ‘yan ta’addar da su ka kai hari kan jirgin ƙasa a ranar 27 Ga Maris, 2022 tsakanin Abuja zuwa Kaduna. Mutum takwas ya mutu a nan take a lokacin kai harin, yayin da aka yi garkuwa da mutum 168. An riƙa sakin mutanen bayan an r...
Kotun majistare dake a Kaduna ta yanke wa Nasiru Yusuf da Tijjani Idris da ake zargi da laifin sace bokatan fenti shida a wani shago hukuncin biyan beli har naira 100,000.

Kotun majistare dake a Kaduna ta yanke wa Nasiru Yusuf da Tijjani Idris da ake zargi da laifin sace bokatan fenti shida a wani shago hukuncin biyan beli har naira 100,000.

Laifuka
Kotun majistare dake a Kaduna ta yanke wa Nasiru Yusuf da Tijjani Idris da ake zargi da laifin sace bokatan fenti shida a wani shago hukuncin biyan beli har naira 100,000. Yusuf mai shekaru 28 da Idris mai shekaru 24 na zama a kauyen Kinkinau ne dake Kaduna. Dan sandan da ya shigar da karar Chidi Leo ya ce Wani Aliyu Shugaba mazaunin titin Ahmadu Bello way ne ya kawo kara a ofishinsu dake Gabasawa ranar 15 ga Afrilu. Leo ya ce Shugaba ya bayyana cewa Yusuf da Idris sun kutsa shagonsa dake titin Taiwo road a Kaduna suka sace bokatan fenti shida da janareta daya duk da aka yi musu kudi naira 185,000. Ya ce Shugaba ya Kuma ce barayin sun saci kofofi guda biyar, katan biyu na tiles din bango da katan biyu na tiles din kasa duk da aka yi musu kudi akan naira 235,000. Leo ya c...