fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Siyasa

Shugaban kasa, Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima zasu kashw Naira Biliyan 15 wajan Tafiye-Tafiye a shekarar 2024

Shugaban kasa, Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima zasu kashw Naira Biliyan 15 wajan Tafiye-Tafiye a shekarar 2024

Siyasa
Tafiye-Tafiye da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima zasu yi a shekarar 2024 zai lashe Naira Biliyan 15.961. Hakan na kunshene a cikin kasafin kudin shekarar 2024 da yanzu haka yake a gaban majalisar tarayya tana tantanceshi. A lokacin gabatar da kasafin kudin a gaban majalisar, shugaba Tinubu yace kasafin kudin zai samar da ci gaban kasa da ayyukan yi.
Kotun ɗaukaka kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya

Kotun ɗaukaka kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya

Siyasa
Kotun ɗaukaka kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Inuwa Yahaya. Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da nasarar gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, a matsayin zaɓabɓen gwamnan jihar Gombe. Kotun mai alkalia uku, dukkansu sun amince cewa jam'iyyar PDP da kuma ADC sun ƙasa tabbatar da zargin da suke yi na aikata ba daidai a zaɓen. Mai shari'a Orji Abadua, wanda ya jagoranci tawagar alkalan da suka yanke hukuncin, sun amince da hukuncin da kotun sauraron korafin zaɓen gwamnan ta yanke, wadda kuma ta kori ƙarar ɗan takarar jam'iyyar PDP, Jibrin Barde.
Bayan da Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da tsige Abba: NNPP ta shigar da kara gaban Kotun Koli kan shari’ar gwamnan Kano

Bayan da Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da tsige Abba: NNPP ta shigar da kara gaban Kotun Koli kan shari’ar gwamnan Kano

Siyasa
Jam'iyyar NNPP mai adawa a Najeriya ta shigar da kara gaban Kotun Kolin kasar inda take kalubalantar hukuncin kotun daukaka kara da ya soke nasarar gwamna daya tilo da jam'iyyar ta samu a zaben watan Maris. NNPP ta shigar da karar ce inda ta kafa manyan hujjoji guda goma, tana neman kotun koli ta sake nazari kan hukuncin karamar kotun sannan ta warware ɓangarorin da suka bai wa Abba Kabir Yusuf rashin nasara. Haka zalika, ta nemi kotun ta tabbatar da bangarorin hukuncin da suka bai wa dan takararta, gwamnan Kano mai ci nasara. Daga cikin bangarorin hukuncin kotun daukaka kara da take kalubalanta kamar yadda wata takardar kotu ta nuna, NNPP ta yi ikirarin cewa sashe na 177 karamin sashe na c, bai fitar da ka'ida a kan kasancewar mutum dan jam'iyya ba. Sannan ta ce wani mutum daban ba sh...
Maganar gaskiya kalar Dimokradiyyar Turawa bata karbe mu ba>>Obasanjo

Maganar gaskiya kalar Dimokradiyyar Turawa bata karbe mu ba>>Obasanjo

Siyasa
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa, Kalar Dimokradiyyar turawa bata karbe mu ba. Yace irin mulkin Dimokradiyya na turawa bai karbe mu ba a matsayin mu na 'yan Afrika. Shugaban yace kalar mulkin bai duba tarihi da al'adar Afrika ba wajan aiwatar dashi. Ya bayyana hakane a wajan wani taro a Abeokuta, jihar Ogun. Yace salon mulkin Dimokradiyyar Turawa bai duba maslahar gaba dayan Al'umma, yana duba amfanin wasu kalilan ne kawai. Yayi kiran a maye kalar mulkin Dimokradiyyar irin na turawa da wanda zai yi daidai da 'yan Afrika.  
Tun bayan cire tallafin man fetur, Yanzu muna samun kudin shiga Tiriliyan 1 duk wata>>Gwamnatin Tarayya

Tun bayan cire tallafin man fetur, Yanzu muna samun kudin shiga Tiriliyan 1 duk wata>>Gwamnatin Tarayya

Siyasa
Gwammatin tarayya ta bayyana cewa, bayan data cire tallafin man fetur a yanzu tana samun kudin shiga da suka kai Naira Tiriliyan 1 duk wata. Ministan kudi, Mr Wale Edun Ne ya bayyana haka. Yace a baya suna samun Naira Miliyan 650 duk wata amma da aka cire tallafin a cikin watanni 4 da suka gabata, suna samun Naira Tiriliyan 1 duk wata. Yace tun tuni dama sun san cewa ba za'a iya ci gaba da biyan Tallafin man fetur din ba. Yace biyan tallafin yasa gwamnati ta na asarar kudaden shiga da yawa.
Da Duminsa: A jihar Filato ma, kamar dai yanda aka yi a Kano, Kotun daukaka kara ta sauke Gwamna Mutfwang inda tace Nentawe na APC ne sabon Gwamna

Da Duminsa: A jihar Filato ma, kamar dai yanda aka yi a Kano, Kotun daukaka kara ta sauke Gwamna Mutfwang inda tace Nentawe na APC ne sabon Gwamna

Siyasa
Kotun daukaka kara dake Abuja ta sauke gwamna Barr. Caleb Mutfwang na jihar Filato, inda ta tabbatar da Nde Nentawe Yilwatda na APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar. Kotun tace jam'iyyar PDP ta saba dokoki da yawa. Ko da a jihar Kano ma dai haka ce ta faru inda kotun daukaka kara ta sauke gwamna meci, Abba Gida-Gida ta baiwa Nasiru Yusuf Gawuna.
Gwamnan Kogi yace akwai munafukai, Maciya amana a tare dashi kuma zai yi maganinsu

Gwamnan Kogi yace akwai munafukai, Maciya amana a tare dashi kuma zai yi maganinsu

Siyasa
Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello ya bayyana cewa, akwai maciya amana a tare dashi kuma zai yi maganinsu.   Gwamnan ya bayyana hakane a yayin ganawa da wasu masu ruwa da tsaki a jam'iyyar APC ta jihar Kogin.   Yace akwai wanda ya musu sha tara ta arziki amma suna munafurtarsa. Yace sai ya tabbatar sun dandana kudarsu.   Rahoton dailypost dai yace gwamna Yahya Bello ya samu tirjiya daga jam'iyyarsa saboda zabar Ododo a matsayin wanda zai gajeshi.
Mun gano masu daukar nauyin kashe-kashen Mutane a Najeriya amma ba zamu kunyatasu ko fadin sunayensu ba>>Gwamnatin Tarayya

Mun gano masu daukar nauyin kashe-kashen Mutane a Najeriya amma ba zamu kunyatasu ko fadin sunayensu ba>>Gwamnatin Tarayya

Siyasa
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, ta gano masu daukar nauyin ta'addanci a Kasar amma ba zata bayyana sunayensu ko kunyata su ba.   Hakan ya fito ne daga bakin ministan shari'a kuma me baiwa shugaban kasa shawara kan shari'a, Mr. Lateef Fagbemi (SAN).   Ya bayyana hakane a Abuja a wajan wani taro kan yaki da satar kudi.   Ya bayyana cewa maganar gaskiya ba zasu bayyana sunayen wanda ke daukar nauyin kashe-kashen ba saboda hakan ka iya kawowa binciken da ake tarnaki.