
Kisan Anambra: ‘Saura kadan na haukace bayan kashe min matata mai ciki da ‘ya’yana huɗu’
Mutumin da aka kashe wa matarsa mai ciki wata tara da kuma ƴaƴansa huɗu a jihar Anambra a kudancin Najeriya, ya ce ya ji kamar ya haukace saboda tashin hankalin da ya shiga.
Wasu ƴan bindiga da ake zargin ƴan ƙungiyar IPOB ne suka kai hari suka kashe mutum 12 da suka ƙunshi mace mai ciki wata tara Harira Jibril da ƴaƴanta huɗu.
Mijin matar kuma mahaifin ƴaƴan dukkanin mata da aka kashe a harin ya shaida wa BBC cewa an kashe matarsa ne da ƴaƴansa a lokacin da suke kan hanyar dawo wa daga ziyarar da ta kai, tare da ƴaƴanta a yankin Orumba ta arewa a jihar Anambra.
"Na shiga tashin hankali, saura kaɗan na haukace - kamar an saka ni cikin wuta, haka nake ji saboda zafin da nake ji," in ji Jibril Ahmed mijin matar da aka kashe da kuma ƴaƴansa huɗu.
"Yanzu ina zan f...