fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Tsaro

Bayan Kwashe kusan watanni 6 tana karyatawa a karshe dai, Hukumar Sojojin Saman Najariya ta amince da kuskuren harba bamabaman da suka kashe farar hula 39 a jihar Nasarawa

Bayan Kwashe kusan watanni 6 tana karyatawa a karshe dai, Hukumar Sojojin Saman Najariya ta amince da kuskuren harba bamabaman da suka kashe farar hula 39 a jihar Nasarawa

Tsaro
Kungiyar kare hakkin bil'adama ta Human Right Watch ta bayyana cewa, hukumar sojojin Saman Najariya ta amince da aikata kuskuren jefa bam a kauyen Kwatiri na jihar Nasarawa da ya kashe mutane farar hula 39. A watan Janairu na shekarar 2023 ne dai aka samu wannan kuskure. Dama dai a baya, Gwamna Abdullahi Sule na jihar ya bayyana cewa, ba sojojin saman Najariya ne suka aikata harin ba inda yace a ranar jirgin saman sojojin Najariya bai yi shawagi a yankin da lamarin ya faru ba. Ya bayyana cewa, harin wani jirgi mara matuki ne da ba'a san wanene ke dashi ba ya kaishi. Hukumar HRW tace tsaiko wajan amincewa da kai harin da sojojin Najariya suka yi bai taimakawa lamarin ba. Tace kuma hukumar sojojin ta baiwa wadanda lamarin ya shafa diyya.
Ƴan sanda sun gano wani gida da ake zargi ana haihuwar jarirai ana sayarwa a jihar Rivers

Ƴan sanda sun gano wani gida da ake zargi ana haihuwar jarirai ana sayarwa a jihar Rivers

Tsaro
Ƴan sanda a jihar Rivers da ke kudu maso kudancin Najeriya sun ceto wasu mata masu juna biyu (ciki) guda shida bayan da su kai sumame a wani gida da ake zargin waje ne da ake haifar jarirai a sayar da su. Rahotanni sun ce jami'an sun kama wata mata mai shekara 39, wadda ake zargin ita ce mai gidan. Kuma ta amsa laifin da ake zarginta da shi na tara matan da gudanar da harkar, inda ta ce ta dade tana yi. A yanzu dai matar da sauran wadanda suke taimaka mata wajen tafiyar da harkar na tsare ana gudanar da karin bincike da nufin kamo sauran wadanda ke da hannu a ciki, kamar yadda kwamishinan ƴan sanda na jihar, Polycarp Emeka, ya sanar. Wannan dai ba wani sabon abu ba ne a Najeriya musamman a yankin kudancin kasar inda ake tara mata a gida suna haihuwa a sayar da jariran. Domin an sha ka...
Mutum huɗu sun mutu a fashewar tukunyar gas a Sokoto

Mutum huɗu sun mutu a fashewar tukunyar gas a Sokoto

Tsaro
Akalla mutum huɗu ne suka rasu sakamakon fashewar tukunyar iskar gas a wani shagon mai akin walda da ke karamar hukumar Isa na jihar Sokoto. Kakakin ƴan sanda a jihar DSP Sanusi Abubakar ya tabbatar wa Gidan Talabijin na Channels cewa fashewar ta auku ne a ranar Lahadi. Sai dai ya ce fashewar ba ta da nasaba da rashin tsaro da ake fama da shi a yankin, illa tukunyar gas ce kawai ta fashe. DSP Sanusi ya ce ba ya ga mutum huɗu da suka rasu, akwai wasu mutum uku da suka jikkata kuma suna karɓar magani a asibiti.
Gwamnatin tarayya ta gargadi cewa kada a rika kalaman da basu dace ba a shafukan sada zumunta har sai an kammala rantsar da Tinubu kuma bakin Turawa da aka gayyata sun tafi

Gwamnatin tarayya ta gargadi cewa kada a rika kalaman da basu dace ba a shafukan sada zumunta har sai an kammala rantsar da Tinubu kuma bakin Turawa da aka gayyata sun tafi

Tsaro
Babban me baiwa shugaban kasa shawara ta fannin tsaro, Babagana Monguno ya bayyana cewa kada a rika kalaman da basu dace ba a shafukan sada zumunta a yayin rantsar da sabon shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu har sai an kammala rantsar dashi din kuma turawa da aka gayyata sun koma gida. Yayi kiran da aka rika amfani da shafukan sada zumunta wajan yada alheri a yayin rantsar da sabon shugaban kasar. Ya bayyana hakane a Abuja a wajan kaddamar da fara shirye-shiryen rantsar da Tinubu. Ya bayar da tabbacin samar da tsaro sosai a yayin bikin rantsar da sabon shugaban kasar.  
Dan Bindiga ya tayar da bam ya kashe kansa a Keke, Kaduna dan kada jami’an tsaro su kamashi

Dan Bindiga ya tayar da bam ya kashe kansa a Keke, Kaduna dan kada jami’an tsaro su kamashi

Tsaro
Lamarin ya faru a Ibrahim Haske Road dake Keke, a Millennium City, Kaduna.   Da safiyar ranar Litinin ne jami'an tsaron suka kai samame yankin inda shi kuma wanda ake zargi ya kwammace ya tayar da bam dake jikinsa ya kashe kansa mamakon a kamashi.   Wasu shaidu sun ce sun ji harbe-harbe da misalin karfe 1 na dare yayin da jami'an DSS dana Sojoji suka je gidan wanda ake zargin.   Da yaga an masa kofar rago shine ya kashe kansa ta hanyar tayar da bom. An kwace Bindigar AK47 a hannunsa sannan an kwance wasu bamabamai da ya dana guda biyu.   Bam din ya tarwatsa jikin mutumin inda kuma aka tafi da matarsa da 'ya'yansa.   Daily Trust tace daya daga cikin masu unguwannin yankin ya tabbatar mata da faruwar lamarin.