fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Tsaro

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mata takwas a Abuja

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mata takwas a Abuja

Tsaro
Rahotanni daga birnin Tarayyar Najeriya, Abuja na cewa an yi garkuwa da wasu mata takwas a yankin Kuje. Wannan labari na zuwa ne kasa da sa'o'i 48 da sace mataimakin shugaban karamar hukumar Kwali da wasu mutane shida a kauyen Yewuti da ke Kwalin. Matan da manoma ne an sace su ne a wata gona da ke kauyen Gwombe da ke masarautar Gwargwada a karamar hukumar Kuje. Wani mazaunin Gwargwada, Usman Yakubu ya shidawa jaridar Daily Trust ta Najeriya cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 5 na yammacin ranar Litinin. Ya kuma kara da cewa wasu 'yan bindiga ɗauke da bindigogi kirar AK-47 ne suka yi awon gaba da matan, wadanda dukkaninsu matan aure ne da ke aikin girbi a gonakinsu. Wani basaraken kauyen da ya zaɓi a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace mutanen, sannan ya zargi cewa maharan 'yan b...
Kuma Dai: An sake baiwa wajan Maulidi hari a jihar Katsina, Mutum daya ya mutu da dama sun jikkata

Kuma Dai: An sake baiwa wajan Maulidi hari a jihar Katsina, Mutum daya ya mutu da dama sun jikkata

Tsaro
A karo na biyu, mahara sun sake kaiwa wajan Maulidi hari a jihar Katsina inda mutum daya ya mutu da dama suka jikkata.   Lamarin ya farune a kauyen Zagami dake karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina.   Jaridar Guardian ta bayyana cewa wani wanda lamarin ya rutsa dashi ya bata labarin cewa, tsakar dare suka fara jin harbe-harbe inda mutane suka rika gudu dan neman tsira.   Yace 'yan Bindigar sun sace mutane da yawa, wasu sun jikkata kuma an kashe mutum daya.   Cikin wadanda aka sace akwai mata da kananan yara da kuma wani malami daga kasar Ghana wanda maulidinne ya kaishi garin.      
Bayan kisan kiyashin da sukawa Falasdinawa dubu Goma sha daya, Yahudawa sun bayyana sharadi daya da zai sa su daina kaiwa Falasdinawan hari

Bayan kisan kiyashin da sukawa Falasdinawa dubu Goma sha daya, Yahudawa sun bayyana sharadi daya da zai sa su daina kaiwa Falasdinawan hari

Tsaro
Shugaban Yahudawan Israila, Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa babu gudu ba ja da baya a yakin da suke da Falasdinawa.   Yace sharadi daya tal da zai sa su daina kashe Falasdinawan shine idan an saki Yahudawan da kungiyar Hamas ta yi garkuwa dasu.   Hakan na zuwane bayan da hare-haren na Yahudawan ya kashe Falasdinawa Dubu Goma Sha Daya.   Kananan Yara sama da Dubu 4 ne suka mutu a wadannan hare-haren.   Netanyahu ya bayyana hakane yayin ziyarar da ya kaiwa wasu sojojin kasar ta Israela.  
Da Duminsa: An kashe Isra’ilawa sama da 600 – Gwamnati

Da Duminsa: An kashe Isra’ilawa sama da 600 – Gwamnati

Tsaro
Sama da Isra'ilawa 600 ne aka kashe tun bayan harin da Falasɗinawa suka kaddamar a ranar Asabar, a cewar gwamnatin ƙasar a wata sanarwa da ta wallafa a shafin Facebook. Ta ƙara da cewa an yi garkuwa da mutum sama da 100, sannan 2,000 sun jikkata. A Gaza, akalla mutum 313 ne aka kashe biyo bayan hare-hare ta sama da Isra'ila ta kai, a cewar jami'an Falasɗinawa.
Hotunan yanda Faladinawa suka yi garkuwa da Babban janar din sojan kasar Israela, Janar Nimrod Aloni

Hotunan yanda Faladinawa suka yi garkuwa da Babban janar din sojan kasar Israela, Janar Nimrod Aloni

Tsaro
Kungiyar Hamas ta sanar da yin garkuwa da daya daga cikin janarorin sojan kasar Israela, janar Nimrod Aloni.   Masu sharhi akan Al'amuran yau da kullum dai sun bayyana cewa wannan babban abin kunyane ga kasar ta Israela.   Janar Nimrod dai shine kwamandan Rundunar soja da ake kira da Depth Corps. Ana sa ran dai Hamas na yin garkuwa da yahudawanne dan tattaunawa akan suma a saki mutanen su da aka kama kamin su saki yahudawan.