
Yadda sojoji suka kashe Gyatuma mai saida tuwo da dukan tsiya saboda dokar Korona
Gidauniyar ‘CLEEN Foundation’ ta fadi yadda sojoji suka kashe wata gyatuma mai tuwo-tuwo da dukan tsiya wai don ta ki zama cikin gida bayan saka dokar Kulle da gwamnatin jihar Nasarawa ta saka.
Da ya ke yi wa PREMIUM TIMES karin bayani shugaban gidauniyar Anna White-Agbo ta shaida cewa sojojin sun fito korar wadanda suka fito a lokacin da aka saka dokar Zaman Gida Dole ne.
” Sojojin sun yi ta korar mutane su koma gida da bulala, da suka tinkari wannan mata ita kuma ta ce ba za ta tafi gida ba sai ta saida abincin domin basu da komai a gida. Daga nan sai suka hau ta da duka har sai da ta mutu.
An ce an sanarwa rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa. Sai dai kuma kakakin rundunar Ramhan Nansel, ya ce bashi da masaniya game da haka.
...