fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Cocin katolik ta bayyana ranar da zata binne mutanen ‘yan bindiga suka kashe a cikin cocin dake jihar Ondo

Cocin katolikawa ta jihar Ondo ta bayyana cewa za a bunne mutanen da ‘yan bindiga suka kashe a cocin katolik dake karamar hukumar Owo ranar juma’a.

Zasu gudanar da jana’izar ne a Otapete, layin Emure da misalin karfe tara na safe.

A ranar lahadi hudu ga watan yuni ne ‘yan bindiga suka kaiwa cocin mummunan hari inda suka kashe mutane dama kuma suka raunana wasu.

Cocin ta kasance a mahaifar gwamnan jihar watau Rotimi Akeredolu inda yace kimanin mutane 40 suka rasu.

 

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *