Kwanakin bayane, jarumar shirin fim dinnan da ake nunawa a gidan talabijin na Arewa24 watau Dadin-Kowa wadda ake kira da Alawiyya tayi aure, ansha biki, jama’a da dama sun tayata murna. Kwatsam sai ga sanarwa daga gidan talabijin din cewa Alawiyyar zata dawo taci gaba da yin shirin fim din na Dadin-Kowa, to da alamadai wannan abu be yiwa mutane dadiba.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Bayan da gidan talabijin din ya fitar da sanarwa a dandalinshi na sada zumunta da muhawara cewa jarumar zata dawo, mutane sunyi ta fadin cewa da aurenta, wasu kuma cewa sukayi gaskiya baku kyautaba.
Ga irin ra’ayoyin da wasu da suka bayyana akan wannan sanarwa ke cewa:
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});