fbpx
Wednesday, March 29
Shadow

DA DUMI-DUMI: Buhari ya umarci jami’an tsaro da su ceto duk wadanda aka yi garkuwa da su

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umurci jami’an tsaro da su kubutar da duk mutanen da aka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na Kaduna da kuma sauran mutanen da ake garkuwa da su.

Mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Babagana Munguno, shine ya bayyana hakan a ranar Alhamis bayan taron majalisar tsaro ta kasa da shugaba Buhari ya jagoranta a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Munguno ya ce shugaban kasar yana jin takaicin matsalar tsaro a kasar, don haka ya bukaci shugabannin tsaro su dauki matakin gaggawa.

Karanta wannan  Hukumar kula da ingancin abinci ta Saudiyya ta kwace tan biyar na naman kaji da ya lalace

Ya kuma yi kira da a karfafa tsaro a iyakokin kasar domin dakile rashin tsaro.

Da sabon umarnin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya baiwa hafsoshin tsaro, ana sa ran nan ba da jimawa ba za a kubutar da wadanda aka sace.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *