fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Da gangan gwamnatin tarayya ta ki magance matsalar tsaro>>Wani Gwamnan Arewa ya fasa kwai

Gwamnan jihar Benue Samuel Ortom ya bayyana cewa, da gangan gwamnatin tarayya ta ki yin maganin matsalar tsaron da ake fama da ita.

 

Ya bayyana hakane yayin da wata kungiyar Turawa daga kasar Ingila suka kai masa ziyara.

 

Yace yana kira ga kungiyoyin Duniya dasu zo su sa gwamnatin tarayya ta magance matsalar tsaron da akw fama da ita ba tare da la’akari da banbancin Addini ko na kabila ba.

 

Ortom ya bayyana hakane a sanarwar da ya fitar ta hannun sakataren yada labaransa, Nathaniel Ikyur.

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *