Kungiyar masoyan Tinubu ta mata ta bukaci dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar APC cewa ya zabi mace a matsayin abokin takararsa.
Inda suka bayyana cewa mata da dama a jam’iyyar APC suna son Tinubu ya mulki Najeriya domin zai kawo sauyi.
Shugabar kungiyar, Bolanle Kazeem ce ta bayyana hakan a babban birnin tarayya yayin da suke zagaye suna wayar da kan mata suyi katin zabe.
Inda tace Tinubu zai kawo sauyi a kasa sosai ta fannin matsalar tsaro da cai sauransu kamar yadda yayi a jihar Legas.