fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Duk Labarai

Za a fara gwajin riga-kafin cutar HIV a Afirka ta Kudu

Za a fara gwajin riga-kafin cutar HIV a Afirka ta Kudu

Uncategorized
Za a fara gwajin riga-kafin cutar HIV a Afirka ta Kudu   Ƙasashen Afirka ta Kudu da Amurka za su fara gwajin riga-kafin cutar HIV, inda suka yi kira ga mutane da su bayar da haɗin kai domin gudanar da gwajin.   Cibiyar bincike ta Amurka (NIH) ta ce an ƙirƙiri sabon riga-kafin mai suna VIR-1388, domin taimaka wa ƙwayoyin jini masu taimaka wa garkuwar jiki da ake kira 'T-cells', waɗanda ke yaƙar sauran ƙwayoyin cutuka da ke kawo wa jiki hari.   Riga-kafin zai taimaka wajen sanya garkuwar jiki ya samar da ƙwayoyin 'T-cells', waɗanda za su iya gano ƙwayar cutar HIV domin sanar da garkuwar jiki, don ya ɗauki matakin kare jiki daga mummunar illar da ƙwayar za ta yi wa jiki.   Cibiyar bincike ta Amurka NIH, da gidauniyar 'Bill and Melinda Gates' da wani...
Ayyana Gawuna matsayin Gwamna ya sa na cire kai na daga sahun ‘yan Nijeriya – Adam

Ayyana Gawuna matsayin Gwamna ya sa na cire kai na daga sahun ‘yan Nijeriya – Adam

Uncategorized
Ayyana Gawuna matsayin Gwamna ya sa na cire kai na daga sahun 'yan Nijeriya - Adam   “Matashi Adam Longbest yace Insha Allahu Gawuna baze taɓa mulkarsa ba saboda baya buƙatar ƙara ganin azzalumar gwamnati irin wacce ya gani ta Ganduje yasan babu abinda zai sauya tsakanin Gawuna da Ganduje duk irin mulkin ɗaya ne.   “Matashin ya ƙara da cewa maganarma ace Gawuna shine yafi ba ta taso ba tunda Allah ba ya goyon bayan zalîncî, kuma kowa yasan zalîncî akayi wajen ayyanasa da kotu ta ce shine ya yi Nasara ta ina? dan haka shidai baiga wanda zai gamsar dashi akan cewa wannan ba azzâlúmâr gwamnati take mulki tun daga sama wannan shiryaiyan abune.   Bugu da ƙari matashi Adam ya ƙara da cewa ba zai taɓa yiwa Azzalumai biyayya ba kan duk mummunar halayayar su, kuma i...
Tsohon gwamnan Kano kuma shugaban jam’iyyar da ke mulkin Najeriya, Dr. Ganduje ya ce a shirye suke da zuwa duk wani mataki na shari’a har sai har Nasir Yusuf Gawuna ya mulki Kano saboda su ke da gaskiya.

Tsohon gwamnan Kano kuma shugaban jam’iyyar da ke mulkin Najeriya, Dr. Ganduje ya ce a shirye suke da zuwa duk wani mataki na shari’a har sai har Nasir Yusuf Gawuna ya mulki Kano saboda su ke da gaskiya.

Uncategorized
Tsohon gwamnan Kano kuma shugaban jam'iyyar da ke mulkin Najeriya, Dr. Ganduje ya ce a shirye suke da zuwa duk wani mataki na shari'a har sai har Nasir Yusuf Gawuna ya mulki Kano saboda su ke da gaskiya. Ina ra'ayinku kan hukuncin kotun farko da ya soke nasarar Gwamna Abba Kabir Yusuf mai ci a yanzu - da ma abin da shugaban APC na kasa ke fadi?
Yaron da hanjinsa ya ɓace a asibitin Legas ya mutu

Yaron da hanjinsa ya ɓace a asibitin Legas ya mutu

Uncategorized
Yaron da hanjinsa ya ɓace a asibitin Legas ya mutu   Wani yaro ɗan shekara 12, mai suna Debola Akin-Bright, wanda a baya aka bayar da rahoton ɓacewar ƴan hanjinsa a asibiti, ya rasu.   Ɗaya daga cikin iyalan yaron ne ya tabbatar wa BBC da hakan, inda ya ce kafin mutuwarsa, yaron ya yi fama da zuban jini a cikin tumbinsa.   Ya ce iyalin sun garzaya da yaron ne zuwa asibiti, inda aka zarce da shi wurin bayar da kulawa ta musamman na Asibitin Koyarwa na Jami'ar jihar Legas, inda a can ne rai ya yi halinsa.   Tun farko yaron dai ya shiga matsanancin hali bayan jerin tiyata da aka yi masa a baya, inda a nan ne aka tabbatar da cewa babu wani ɓangare na hanjinsa.   A tattaunawar da ta yi da BBC, a farkon watan Satumba, mahaifiyar yaron, Mrs D...
Hedikwatar tsaron Najeriya za ta yi bincike kan ‘bidiyon ƴan bindiga a Katsina’

Hedikwatar tsaron Najeriya za ta yi bincike kan ‘bidiyon ƴan bindiga a Katsina’

Uncategorized
Hedikwatar tsaron Najeriya za ta yi bincike kan 'bidiyon ƴan bindiga a Katsina'   Hedikwatar tsaron Najeirya ta ce ta kaddamar da bincike kan wani bidiyo da ya yadu a shafukan sada zumunta da ke nuna wasu da ake zargin sojoji ne suna magana da wasu mutane a kan babura ɗauke da makamai, waɗanda ake tunanin ƴan fashin daji ne.   Ana zargin cewa, an ɗauki bidiyon ne a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.   A cikin bidiyon an ji wani da ba a san ko wane ne ba, na bayyana cewa "an yi sulhu da mutanen kuma za a bar su, su wuce ba tare da an taɓa su ba."   Wata sanarwa da mai magana da yawun hedikwatar tsaron ta Najeriya, Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar, hedikwatar ta ce maƙasudin gudanar da binciken shi ne a tabbatar da sahihancin bid...
Farashin ɗanyen man fetur ya yi tashin da bai taɓa yi ba cikin wata goma

Farashin ɗanyen man fetur ya yi tashin da bai taɓa yi ba cikin wata goma

Uncategorized
Farashin ɗanyen man fetur ya yi tashin da bai taɓa yi ba cikin wata goma Getty ImagesCopyright: Getty Images Farashin man fetur a duniya ya yi tashin da bai taɓa yi ba a cikin watanni goma. Farashin gangar ɗanyen mai na Brent ya tashi zuwa sama da dalar Amurka 95 a ranar Talata. Tashin farashin ya zo ne bayan rage yawan ɗanyen man fetur da ƙasashe biyu mafiya fitar da man fetur ɗin suka yi, wato Saudiya da kuma Rasha. Hukumar kula da makamashi ta duniya ta yi gargadin cewa ɗanyen man zai yi ƙaranci nan da ƙarshen shekara. Farashin man fetur ya tashi zuwa dalar Amurka 120 kan kowace ganga bayan mamayen da Rasha ta ƙaddamar kan Ukraine a shekarar da ta wuce, sai dai ya sauko zuwa dalar Amurka 70 a cikin
Hukumomi sun shawarci ƴan Afirika ta kudu su riƙa wankan minti biyu

Hukumomi sun shawarci ƴan Afirika ta kudu su riƙa wankan minti biyu

Uncategorized
Hukumomi sun shawarci ƴan Afirika ta kudu su riƙa wankan minti biyu AFPCopyright: AFP Hukumomin samar da ruwa a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, sun bukaci mazauna birnin da kewayen da su taƙaita yawan ruwan da suke amfani da shi sakamakon karancin ruwa da ake fama da shi wanda zai iya haifar da durƙushewar al'amura. Kamfanonin samar da ruwa na 'Rand' da 'Johannesburg' a ranar Lahadin da ta gabata sun ce yawan ruwan da mazauna yankin ke amfani da shi "yana kawo cikas ga tsarin samar da ruwa" kuma ya haifar da ƙarancinsa a rumbun adana ruwan. Kamfanonin sun buƙaci mazauna yankin da su taƙaita wanka zuwa mintuna biyu bayan haka, kada su yi amfani da ruwa sai idan sun yi ba-haya, kuma su kiyayi wanke motoci har sai karshen mako-mako, su guji amfani da ruw...
SERAP ta maka Tinubu a kotu kan alawus ɗin wasu ministoci

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan alawus ɗin wasu ministoci

Uncategorized
SERAP ta maka Tinubu a kotu kan alawus ɗin wasu ministoci Ƙungiyar kare hakkin ƴan ƙasa da tabbatar da shugabanci na gari a Najeriya 'SERAP’ ta kai ƙarar shugaba Bola Tinubu kotu kan gazawar sa wajen hana tsofaffin gwamnonin da suke rike da mukamin minista karbar kudaden fansho na jihohi.   Kungiyar SERAP dai na neman kotu ta tilasta wa Tinubu ya umarci wadannan tsofaffin gwamnonin da su daina karbar irin wadannan kudade.   A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ranar Lahadi, mataimakin shugaban ƙungiyar a Najeriya, Kolawole Oluwadare, ya ce ministocin da abin ya shafa su ne Nyesom Wike da Bello Matawalle da Adegboyega Oyetola.   Sauran tsofaffin gwamnonin sun hada da Badaru Abubakar da David Umahi da Simon Lalong da Atiku Bagudu da kuma Ibrahim Geidam. ...
Rundunar ƴansanda a jihar Katsina ta bukaci al’umma da su yi watsi da wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta na zargin karkatar da kayan tallafin abinci da jami’anta ke yi.

Rundunar ƴansanda a jihar Katsina ta bukaci al’umma da su yi watsi da wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta na zargin karkatar da kayan tallafin abinci da jami’anta ke yi.

Uncategorized
Rundunar ƴansanda a jihar Katsina ta bukaci al’umma da su yi watsi da wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta na zargin karkatar da kayan tallafin abinci da jami’anta ke yi. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, PPRO, ASP Aliyu Abubakar Sadiq ya fitar. Rundunar ƴansandan ta ce faifan bidiyon ba kawai yaudara ba ne, an fitar da shi ne da nufin bata sunan ƴansanda. “Bayan cikakken bincike, an gano cewa buhunan shinkafar da aka gani a bidiyon a cikin motar ‘yansanda an kama su ne daga hannun wasu ɓatagari. “Wasu marasa gaskiya sun yi samu fiye da kason su na kayan agajin , shine ƴansanda suka kama suka kuma mayar da su wurin da aka raba. “Saboda haka abinda bidiyon ta nuna ba shi bane gaskiyar lamari kuma yunƙuri ne na k...