fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Duk Labarai

Maguire zai bar Manchester United

Maguire zai bar Manchester United

Wasanni
Dan wasan Manchester United, Harry Maguire zai bar kungiyar.   Maguire wanda shine kaftin din Manchester United ya amince ya bar kungiyar bayan kwashe shekaru a cikinta.   A shekarar 2019 ne dai Harry Maguire ya je kungiyar ta Manchester United akan farashin fan Miliyan €78.3.   Duk da Maguire na shirin barin Manchester United, har yanzu bai samu kungiyar da zata daukeshi ba.        
Shin da gaske Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin Najariya? Hukumar Kwastam ta yi bayani akan hakan

Shin da gaske Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin Najariya? Hukumar Kwastam ta yi bayani akan hakan

Siyasa
Kwamandan Kwastam dake jihar Ogun yayi magana akan yada jita-jitar cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya ce a bude iyakokin Najariya.   Bamidele Makinde Yace tun shekarar data gabata ne aka bude iyakar wadda aka ga mutane na ta murna, sabanin bidiyon da ake yadawa a yanzu a kafafen sadarwa dake nuna cewa yanzu ne aka bude iyakar.   A shekarar 2019 ne dai a watan Augusta tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin kulle iyakokin Najariya domin karfafa noma da samar da kayan amfani a gida da kuma dakile fasa kwaurin kaya.   A shekarar 2020 ne dai shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin bude iyakokin Seme dake Legas, Illela dake Sokoto, Maigatari dake Jigawa, da kuma Mfum dake Cross River.   A shekarar 2022 kuma shugaba ...
Dalibai a kasar China na biyan Naira Dubu 43,000 a kowanne awa dan a koyar dasu yanda ake murmushi

Dalibai a kasar China na biyan Naira Dubu 43,000 a kowanne awa dan a koyar dasu yanda ake murmushi

Uncategorized
Bayan kwashe shekaru suna saka takunkumin fuska saboda zuwan cutar Coronavirus.   Dalibai a kasar Japan na sake koyan yanda ake murmushi.   Kafar Mailonline tace, kamfanin me koyar da murmushin, Keiko Kawano’s company, Egaoiku yace mutane dake zuwa ya rika koyar dasu yanda ake murmushi na ta karuwa.   Koyar da murmushi dai ya zama abin yi a kasar ta Japan inda mutane ke yinsa dan dawowa daidai da rayuwarsu saboda dadewa suna saka takunkumin Fuska.
Bayan Kwashe kusan watanni 6 tana karyatawa a karshe dai, Hukumar Sojojin Saman Najariya ta amince da kuskuren harba bamabaman da suka kashe farar hula 39 a jihar Nasarawa

Bayan Kwashe kusan watanni 6 tana karyatawa a karshe dai, Hukumar Sojojin Saman Najariya ta amince da kuskuren harba bamabaman da suka kashe farar hula 39 a jihar Nasarawa

Tsaro
Kungiyar kare hakkin bil'adama ta Human Right Watch ta bayyana cewa, hukumar sojojin Saman Najariya ta amince da aikata kuskuren jefa bam a kauyen Kwatiri na jihar Nasarawa da ya kashe mutane farar hula 39. A watan Janairu na shekarar 2023 ne dai aka samu wannan kuskure. Dama dai a baya, Gwamna Abdullahi Sule na jihar ya bayyana cewa, ba sojojin saman Najariya ne suka aikata harin ba inda yace a ranar jirgin saman sojojin Najariya bai yi shawagi a yankin da lamarin ya faru ba. Ya bayyana cewa, harin wani jirgi mara matuki ne da ba'a san wanene ke dashi ba ya kaishi. Hukumar HRW tace tsaiko wajan amincewa da kai harin da sojojin Najariya suka yi bai taimakawa lamarin ba. Tace kuma hukumar sojojin ta baiwa wadanda lamarin ya shafa diyya.