Gwamnonin Najariya 36 na can suna ganawa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a fadarsa dake Abuja.
Tinubu ya fara ganawa da gwamnonin ne bayan rantsar da George Akume a matsayin sakataren gwamnatinsa.
Dan wasan Manchester United, Harry Maguire zai bar kungiyar.
Maguire wanda shine kaftin din Manchester United ya amince ya bar kungiyar bayan kwashe shekaru a cikinta.
A shekarar 2019 ne dai Harry Maguire ya je kungiyar ta Manchester United akan farashin fan Miliyan €78.3.
Duk da Maguire na shirin barin Manchester United, har yanzu bai samu kungiyar da zata daukeshi ba.
Lionel Messi zai koma Inter Miami, An yanke shawarar kuma za'a sanar da komawar l shi a cikin sa'o'i masu zuwa.
Messi zai buga MLS a kakar wasa mai zuwa. Babu sauran dama ga Barcelona duk da kokarin ganin daukarsa ya faru.
Daga: [Fagen Wasanni]
Wasu 'yan Achaba a kasar Kamaru na zanga-zangar cire tallafin Man Fetur a Najeriya.
Lamarin ya farune a garin Garoua inda matasan 'yan achaban suke magana da fulatanci da faransa suna sukar shugaba Bola Ahmad Tinubu kan wannan mataki.
https://www.youtube.com/watch?v=yk61qHZN89c
An kama wani barawo a barikin sojojin da ba'a bayyana sunansa ba.
Barawon dai ya wuce sojoji masu tsaro inda ya shiga cikin barikin da niyyar sata, saidai dubunsa ta cika.
Kuma an kamashi:
Kalli Bidiyonsa a kasa:
https://www.youtube.com/watch?v=vGmbE3cFNGY
Kwamandan Kwastam dake jihar Ogun yayi magana akan yada jita-jitar cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya ce a bude iyakokin Najariya.
Bamidele Makinde Yace tun shekarar data gabata ne aka bude iyakar wadda aka ga mutane na ta murna, sabanin bidiyon da ake yadawa a yanzu a kafafen sadarwa dake nuna cewa yanzu ne aka bude iyakar.
A shekarar 2019 ne dai a watan Augusta tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin kulle iyakokin Najariya domin karfafa noma da samar da kayan amfani a gida da kuma dakile fasa kwaurin kaya.
A shekarar 2020 ne dai shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayar da umarnin bude iyakokin Seme dake Legas, Illela dake Sokoto, Maigatari dake Jigawa, da kuma Mfum dake Cross River.
A shekarar 2022 kuma shugaba ...
Kungiyar Real Madrid ta kammala sayen dan wasan kasar Ingila daga kungiyar Borussia Dortmund, Jude Bellingham.
Madrid ta sayeshi ne akan Miliyan €100 kuma ya saka hannu kan kwantirakin shekaru 6.
Wannan ciniki nasa na daya daga cikin manyan cinikin da kungiyar ta Real Madrid ta yi, kuma nan da 'yan kwanaki zai kammala gwajin lafiya a kungiyar.
Bayan kwashe shekaru suna saka takunkumin fuska saboda zuwan cutar Coronavirus.
Dalibai a kasar Japan na sake koyan yanda ake murmushi.
Kafar Mailonline tace, kamfanin me koyar da murmushin, Keiko Kawano’s company, Egaoiku yace mutane dake zuwa ya rika koyar dasu yanda ake murmushi na ta karuwa.
Koyar da murmushi dai ya zama abin yi a kasar ta Japan inda mutane ke yinsa dan dawowa daidai da rayuwarsu saboda dadewa suna saka takunkumin Fuska.
Kungiyar kare hakkin bil'adama ta Human Right Watch ta bayyana cewa, hukumar sojojin Saman Najariya ta amince da aikata kuskuren jefa bam a kauyen Kwatiri na jihar Nasarawa da ya kashe mutane farar hula 39.
A watan Janairu na shekarar 2023 ne dai aka samu wannan kuskure.
Dama dai a baya, Gwamna Abdullahi Sule na jihar ya bayyana cewa, ba sojojin saman Najariya ne suka aikata harin ba inda yace a ranar jirgin saman sojojin Najariya bai yi shawagi a yankin da lamarin ya faru ba.
Ya bayyana cewa, harin wani jirgi mara matuki ne da ba'a san wanene ke dashi ba ya kaishi.
Hukumar HRW tace tsaiko wajan amincewa da kai harin da sojojin Najariya suka yi bai taimakawa lamarin ba.
Tace kuma hukumar sojojin ta baiwa wadanda lamarin ya shafa diyya.
Dan wasan Chelsea, Ngolo Kante ya amince ya koma kungiyar Al-itihad ta kasar Saudiyya.
Fabrizio Romano ya bayyana cewa, Kante ya amince ya koma kungiyar ne har na tsawon shekaru 2.
Kante zai hade da Benzema a kungiyar inda zai rika karbar Albashin Miliyan €100 a wata.