fbpx
Friday, March 31
Shadow

Duk Labarai

Wata baiwar Allah ta ceci rayuwar wasu yara almajirai sun koma makaranta, ta baiwa iyayensu sana’a

Wata baiwar Allah ta ceci rayuwar wasu yara almajirai sun koma makaranta, ta baiwa iyayensu sana’a

Uncategorized
Wannan labarin wata baiwar Allah ce me suna Sera Yusuf wadda ta tallafawa wasu yara masu yin bara da iyayensu, yaran suka daina bara suka koma makaranta sannan iyayen yaran suka samu sana'ar yi. Sera ta kasance tana da shagon da take kasuwanci kuma kullun idan zata wuce bakin wata mahada tana ganin wasu yara guda biyu namiji da mace tana basu sadaka, da yaran suka lura da Sera na basu sadaka kullun sai suka nemi shagonta, wata rana tazo ta ajiye motarta zata shiga shago sai suka rugo suna rokonta "dan Allah ki bamu sadaka mu sayi abinci". Koda Sera taga haka sai ta kirasu cikin shagonta tace musu tana so ita dasu su zama abokai, sukace mata sun yarda, ta tambayesu sunayensu yarinyar tace sunanta A'isha shi kuma yaron yace sunanshi Abdullahi, ta tambayesu shekarunsu A'isha shekararta ...

Tallar maganin bera: “sun kori shugaban kasa, karku bari kuma su koreku”

Uncategorized
Wannan wata tallar maganin berane da akeyi a garin Legas inda masu maganin sukayi amfani da sanarwar da fadar shugaban kasa suka ta bayar kan cewa beraye sun hana shugaba Buhari shiga Ofis dinshi wajan yin tallar, bayan hoton beran da kuke gani a jikin tallar an kuma rubuta da turanci cewa "sun kori shugaban kasa, kar ku bari kuma su koreku". Wannan salo na tallar maganin bera jaha hankulan mutane a inda wasu abin ya basu dariya wasu kuma cewa sukayi wannan renine ga fadar shugaban kasar.
Jaruman fim din hausa sun kaiwa marasa lafiya ziyara a Asibitoci

Jaruman fim din hausa sun kaiwa marasa lafiya ziyara a Asibitoci

Uncategorized
Tawagar tsoffi jaruman fin din hausa da wandanda ake damawa dasu a yanzu karkashin jagorancin tsohuwar jaruma matar Sani Musa Danja, Zakin 'yan wasan Arewa wato Mansurah Isah suna zagayen duba marasa lafiya a asibitocin dake jihar Kano da kai musu kayan agaji. Mansurah itace madugar wannan tafiya sannan tana tattara irin gudummuwar da mutane suka bayar karkashin wata gidauniya data kafa sai a kaiwa marasa marasa lafiya kayan agaji, wannan aikin alheri da sukeyi muna fatan Allah ya sakamusu da mafiyinshi.

Sanata Kanti Bello ya rasu

Uncategorized
Innalillahi wa Inna ilahi raji'un, Allah ya yiwa tsohon dan majalisar dattijai, Sanata Kanti Bello rasuwa da safiyar yau a garin Abuja, shekarun Sanata kanti  72 a Duniya kuma yayi siyasa karkashin jam'iyayyar PDP, muna fatan Allah ya gafartamishi. 
Jamila Nagudu ta zama jakadiyar sabulun Sabil

Jamila Nagudu ta zama jakadiyar sabulun Sabil

Uncategorized
Fitacciyar jarumar fim din hausa, Jamila Umar, Nagudu ta zama meyiwa sabulun Sabil talla, jarumar dai na kara samun cigabane ta bangaren samun karbuwa gurin kamfanoni dake daukarta domin tayi musu tallar hajojinsu domin a yanzu haka Jamila tana yiwa kamfanin magi na Vedan talla kuma sai ga wannan, muna mata fatan alheri da kuma Allah ya kara daukaka.