fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Duk wanda aka kama yana tattaunawa da ‘yan bindinga zamu hukunta shi – Gwamnatin Jihar Kaduna

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce ba ta taba sanya wata kungiya ko wani mutum da zai tattauna a madadin ta da ‘yan bindinga ba.

Kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida, Mista Samuel Aruwan, wanda ya bayyana hakan a jiya, ya yi gargadin cewa duk wanda aka kama yana tattaunawa da ‘yan bindinga a madadin gwamnati za a hukunta shi.

Kwamishinan a cikin wata sanarwa, mai taken ‘Babu wata tawaga da Gwamna El-Rufai ya nada don tattaunawa da yan bindinga, ‘ya ce: jita jita da ake yadawa a wasu kafafen watsa labarai na cewa Gwamnatin Jihar ta nada kwamitin tattauna da yan bindinga ba gaskiya bane.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *