Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya kaddamar da rukunin shagunan ‘yan Tebura dake kasuwar Kantin Kwari wadanda aka gina akan zunzurutun kudi, naira biliyan biyar, wannan guri dai yana daya daka cikin ayyukan da aka tsara cewa shugaban kasa, Muhammadu Buhari zai kaddamar dasu lokacin ziyararshi da ya kai jihar.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Amma saboda karancin lokaci da kuma ayyuka da sukawa shugaban kasar yawa, aka kayyade yawan ayyukan da zai kaddamar din, tun asali dai ayyuka goma sha hudune gwamnatin jihar ta yi, amma yanzu gwamna Ganduje na kaddamar dasu daya bayan daya.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});