fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana matukar Kaduwa game da mutuwar tsohon Ministan Shari’a Abdullahi Ibrahim (SAN)

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya bayyana matukar kaduwa game da mutuwar tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya Abdullahi Ibrahim (SAN), yana mai bayyana rasuwarsa a matsayin rashi ne ga kasar da jihar baki daya.

Mirgayin Dan kabilar Igala ne wanda ya fito daga yankin gabashin jihar Kogi, ya rasu ne a ranar Lahadi 24 ga watan Janairun 2021, kuma shine SAN na farko daga Arewacin Nijeriya haka kuma ya yi aiki a matsayin Babban Lauyan Tarayya A tsakanin shekarar Alif 1997 da kuma Alif 1999.

Karanta wannan  Tinubu ya gana da sarakunan gargajiya a fadarsa

Sakon ta’aziyyar ya fito ne daga bakin, Babban Sakataren yada labaran na gwamna Bello, Onogwu Muhammed wanda ya fitar, inda ya bayyana marigayin Abdullahi a matsayin kwararren masanin shari’a kuma mai aiki da kwarewa.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *