fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello yayi ikrarin cewa nan bada jimawa ba gwamnonin jam’iyyar PDP 10 zasu canza sheka zuwa jam’iyyarsa ta APC

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana cewa kwanan nan wasu abokanan sa gwamnonin PDP zasu kama jam’iyyar APC.

 

Da yake zantawa da tashar talabijin ta Channel Gwamna Yahaya Bello ya bayyana cewa nan gaba kadan wasu abokanan sa gwamnonin jam’iyyar Adawa ta PDP su akalla 10 zasu dawo jam’iyyarsa mai mulkin Najeriya wato APC.

 

Da yake mayar da amsar tambayar cewa ko shin jama’iyyar APC zata durkushe bayan Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar kujerar mulki a shekarar 2023, sai ya ce kokadan illama jam’iyyar APC zata kara karfine.

Karanta wannan  Hotuna: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana sa Kwankwaso

 

Haka zalika Gwamnan ya bayyana takaicin sa na ficewar gwamnan jihar Edo Obadeki daga jam’iyyar APC inda ya sha al’washin cewa lalle nan gaba zaiyi komayya cikin jam’iyyar sa ta asali APC.

 

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *