fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Gwamnatin Buhari ta baiwa iyalan insfeto na jami’an farar hula daya mutu a harin Kuje naira miliyan 2.8

Gwamnatin tarayya ta baiwa iyalan insfeto na hukumar farar hula, Ilyasu Abraham naira miliyan 2.8 bayan daya mutu a harin da ‘yan Boko Haran suka kaiwa gidan kurkuku na Kuje.

A ranar biyar ga watan Yuli ne Abraham ya rasa rayuwarsa yayin dayake kan aikinsa na taimakawa kasarsa ta Najeriya a babban birnin tarayya.

Hukumar ta basu wannan kudin ne a jiya ranar alhamis kamar ta bayyana, inda kwamanda Ahmad Audi ya basu Cheque na naira miliyan 2.5 da kuma kudi naira 300,000.

Kuma a karshe yace zasu dauki diyarsa aiki wato Abimiku Abraham a daliban da zasu dauka aiki na gaba, domin su taimaka iyalan nashi.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *