fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

Gwamnatin jihar Abia ta garkame Otal sama da 4 sakamakon kin bin ka’idojin cutar Korona mai saurin yaduwa

Kimanin otal biyar da ke yankin karamar hukumar Aba ta Arewa A Jihar Abia Jami’an dake sanya ido kan bin laduban cutar Coronavirus a jihar ne suka kulle.

Rahotanni sun bayyana cewa an garkame Otal-Otal din sabuda sakacin masu su na kin bin umarnin gwamnati data sanya kan cutar Covid-19.

Wata majiya ta bayyana cewa wadanda suka ki bin umarnin gwamnatin jihar a kan COVID-19 za a kama su kuma a gurfanar da su a kotun tafi da gidanka.

A halin yanzu, gwamnatin jihar Abia ta haramta duk wasu tarukan dare da ayyukan al’adu a jihar.

Karanta wannan  Matsalar rashin kudi ta fara haifarwa da 'yan Najeriya tabin kwakwalwa, cewar likitan kwakwalwa

Haka zalika shugaban kwamitin dake yaki da cutar a jihar . Chris Ezem ya gargadi mamallakan otal din jihar da su kiyaye matakan kariya na cutar idan bahaka ba zasu fuskanci tara har ta kimanain dubu 100

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *