fbpx
Friday, June 9
Shadow

Gwamnatin tarayya tace matsalar tsaro bata shafi harkar noma sosai ba a kasar Najeriya

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro bata shafi harkar noma sosai ba a kasar Najeriya.

Ministan noma Abubakar Muhammad ne ya bayyan hakan a taron mako-mako da suke gudanarwa a fadar shugaban kasa a babban birnin tarayya.

Inda yace Najeriya itace kasa ta farko da tafi kowace kasa nomar shinka a nahiyar Afrika, sannan kuma itace ta hudu a Duniya bakidaya.

Ya kara da cewa tabbas matsalar tsaro ta shafi harkar noma musamman a arewacin Najeriya, amma ba sosai ba kuma har yanzu ana noma a Najeriya.

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *