A dazune Muka kawo muku labarin yanda gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya zargi makiyan APC da daukar Nauyin ‘yan Bindiga dan bata mulkin jam’iyyar.
Yace masu son tsayawa takara a shekarar 2023 ne ke daukar nauyin ‘yan Bindigar.
Saidai a martaninsa, Sanata Shehu Sani ya wallafa a shafinshi na sada zumunta inda yace A kamar yanda ake kai hare-hare a jihohin APC, A jihohin da PDP ma ke mulki ana kai irin wadannan hare-haren dan haka kada gwamnan ya bada wani uzuri game da gazawarsa.
To Governor Masari;Bandits are killing in PDP controlled states of Sokoto,Zamfara and Benue;Bandits are Killing in APC controlled states of Niger,Kaduna and Katsina;Thou shalt not maketh excuses when thee hath failed.
— Senator Shehu Sani (@ShehuSani) July 20, 2020
Sanata Sani ya bayyana hakane ta shafinshi na sada zumunta.