fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Hukumar farar hula zata dauki yarinyar shugabansu aiki wanda aka kashe a harin kurkukun Kuje

Kwamandan hukumar farar hula, Ahmad Audi ya bayyana cewa zasu dauki Abimiku Abraham, wato yarinyar shugabansu wanda ya rasa ransa a harin kurkukun Kuje.

Ilyasu Abraham ya mutu ne a ranar biyar ga watan Yuli yayin da ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai hari gidan kurkuku na Kuje dake babban birnin tarayya.

Wanda a jiya hukumar ta baiwa iayalansa naira miliyan 2.8 kuma tayi masu albishir cewa zata dauki ‘yarsa aiki a sabbin ma’aikatan da zata dauka na gaba.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *