‘Yan daba sun kaiwa hukumar zabe hari a Surulere dake jihar Legas inda har wni bideyo ya rika yawo cewa sun sace injinan da ake yiwa mutane katin zabe.
Amma hukumar tace tabbas an kai harin sai dai ba a sace masu inji ko daya ba amma sun tashi a wurin sun koma wani wuri na daban don cigaba da yiwa mutane rigista.
Sannan hukumar ta baiwa mutane kan wannan harin da aka kai mata tace zatayi iya bakin kokarinta ta cigaba da yi masu rigistar.