fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Hukumar zabe zata karawa ‘yan Najeriya lokaci don su cigaba da rigistar katin zabe, cewar Mahmood Yakubu

Shugaban hukumar zabe ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa hukumar zata tsawaita lokaci don a cigaba da yin rigistar katin zabe.

A ranar 30 ga watan yuni ne hukumar tace zata daina yin rigistar, amma yanzu tace zata kara lokacin bayan kungiyoyi da dama sun bukaci hakan kamar SERAP da sauran su.

A ranar juma’a ne ya bayyana hakan a babban birnin tarayya Abuja, kuma yace zasu fara ba mutne katin zaben a watan oktoba.

Sai dai ba fadi tsawon lokacin da suka kara ba.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *