fbpx
Wednesday, March 29
Shadow

Idan na zama shugaban kasa, Sai Najeriya ta yi gasa da kasar Japan>>Orzu Kalu

Dan takarar neman shugabancin Najeriya a jam’iyyar APC, Orzu Kalu ya bayyana cewa, idan ya zama shugaban kasa, zai mayar da Najeriya tana gasa da kasar Japan wajan ci gaba.

 

Kalu ya bayyana cewa babu wanda yafi cancantar zama shugaban kasa kamarshi saboda a yanzu haka akwai ‘yan Najeriya 13,000 dake cin abinci a karkashinsa.

 

Ya bayyanawa manema labarai cewa cikin shekaru 4 zai farfado da tattalin arzikin Najeriya.

 

Yace zai karfafa tattalin arzikin Najeriya ya rika gasa dana kasashen Amurka da Japan.

Karanta wannan  Gwamnatin tarayya ta kaddamar da Enterprenuership Programme domin tallafawa ma'aikata da 'yan bautar kasa su samu sana'o'i

 

Yace duk me neman takarar shugabancin Najeriya ya kamata yana iya sanya mutane farin ciki kuma zai iya magance matsalar tsaro.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *